• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Editoci: Tinubu Ya Nemi ‘Yan Jarida Da Yaɗa Ingatattun Labarai Don Jawo Masu Zuba Jari A Nijeriya

by Sulaiman
2 years ago
Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nemi kafafen yaɗa labarai da su taimaka wajen bada labarai da bayanai da za su kyautata matsayin Nijeriya a idon duniya ta yadda masu zuba jari za su samu ƙwarin gwiwar saka dukiyarsu a ƙasar wanda hakan zai taimaka wa cigaban tattalin arzikinta.

Shugaban ya yi wannan kiran ne a saƙonsa da Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya karanta a madadinsa a wajen buɗe Babban Taro na 19 na Dukkan Editocin Nijeriya wanda Ƙungiyar Editocin Nijeriya (NGE) ta shirya a Uyo, Jihar Akwa Ibom, a ranar Laraba.

  • Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka
  • Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

A cikin sanarwar da mai taimakawa ministan na musamman a bangaren yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim, ya bayar a Abuja, ya ruwaito Tinubu ya na faɗin: “An san rawar da ku ke takawa a matsayin tushen farko na labarai kuma masu wayar da kan al’umma game da abubuwan da ke faruwa a fagen tattalin arziki. Don haka, bada rahotanni a kan kari waɗanda babu ƙarin gishiri cikinsu yana taimakawa ga masu sana’o’i su yanke shawarar da ta dace, kuma ya na samar da kyakkyawan yanayi don haifar da cigaban ƙasa.

“Ina kira a gareku da ku samar da kyawawan labarai waɗanda za su bada ƙwarin gwiwa ga masu zuba jari kuma su jawo irin jarin da zai inganta haɓakar tattalin arziki a wannan ƙasa tamu.

“Rawar da kafafen watsa labarai ke takawa wajen samar da kyakkyawan yanayin hada-hadar kasuwanci ta na taimakawa ga daidaita harkar kasuwanci.”

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

Shugaban ƙasar ya ce samar da kyakkyawan musayar ra’ayi kan yadda za a inganta tsarin tattalin arzikin ƙasa wani abu ne da gwamnatin sa ta yi amanna da shi, kuma ya yi kira da a samu haɗin kan editocin wajen ƙoƙarin yin tattaunawa daidai da Manufar Sabuwar Alƙibla ta gwamnatin sa.

Tinubu, wanda ya yi la’akari da matsalolin da ake ciki waɗanda janye tallafin man fetur ya haifar, ya ce gwamnatin sa ta na ɗaukar duk wani mataki da ya dace don rage raɗaɗin da ake ji, ta hanyar tsare-tsare da aka yi da za su kawo sauƙi a cikin ƙanƙanen lokaci, a yayin da ƙasar ta ke jiran ta ci moriyar abin a nan gaba.

Ya lissafa wasu daga cikin tsare-tsaren rage raɗaɗin da su ka haɗa da ƙarin albashi na N35,000 a kowane wata har tsawon watanni shida, wanda ƙari ne kan albashi mafi ƙaranci na Gwamnatin Tarayya; da kafa Asusun Tallafin Ayyuka ga Jihohi don zuba kuɗi a muhimman sassa wanda zai samar da yanayin da zai bunƙasa harkokin kasuwanci, da kuma ƙaddamar da shirin sawo motocin safa-safa samfurin CNG na naira biliyan 100, masu aiki da hasken rana, da kuma kafa Kwamitin Shugaban Ƙasa don tabbatar da aiwatar da shirin.

Ya ce: “Da yake an rattaba hannu kan dokar Ɗorin Kasafin Kuɗi na 2023, mun kammala matakan da za mu bi mu fara biyan kuɗin Tiransifar Tsabar Kuɗi N25,000 ga kowane mutum a cikin mutum miliyan 15 mafi fatara da kuma gidaje waɗanda su ka fi buƙata a Nijeriya, har tsawon wata uku.

“An bada umurnin shugaban ƙasa na fitar da tan 200,000 na hatsi daga rumbunan musamman na gwamnati ga gidajen jama’a a jihohi 36 da gundumar Abuja a farashi mai rahusa, da tan 225,000 na takin zamani, da iri, da sauran kayan aiki ga manoma.”

Tinubu ya ce a dalilin faɗuwar tarbiyya da aka samu a tsawon lokaci, wanda ya jawo raguwar mutunta ƙasa, Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai ta Tarayya (FMINO) ta na nan ta na tsara sauya labarin da ake yaɗawa game da ƙasar nan ta hanyar aiwatar da wani gagarumin shirin wayar da kan al’umma wanda nufin sa ya samar da haɗin kai, kishin ƙasa, da saka shauƙin son al’adun mu a zukatan ‘yan Nijeriya.

Shugaban ƙasar ya yi kira ga dukkan editocin kafafen yaɗa labarai da su yaƙi muguwar ɗabi’ar yaɗa labaran ƙanzon kurege, da labaran yaudara, da labaran ƙarya, masu yin barazana ga al’umma, ya ce su riƙa binciken gaskiyar lamari, da bada labarai cikin hankali da natsuwa, da inganta ilimin aikin jarida da ilimin kafafen zamani.

Ya yaba wa jigogin da su ka kafa ƙungiyar ta NGE, bisa jagorancin marigayi Alhaji Lateef Kayode Jakande, wanda zaƙaƙurin ɗan jarida ne da ake girmamawa kuma har ya riƙe muƙamin Gwamnan Jihar Legas, wanda a cikin 1961, shi da wasu, su ka kafa ƙungiyar, su ka bada gudunmawa ga cigaban ƙasa ta fuskar zamantakewa da siyasa, musamman wajen ‘yanto Nijeriya daga baƙin mulki irin na soja har aka samar da mulkin dimokiraɗiyya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
TCN
Labarai

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
Next Post
Malam Rabi’u Aminu Ya Zama Sabon Babban Limamin Jere

Malam Rabi’u Aminu Ya Zama Sabon Babban Limamin Jere

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal

October 9, 2025
Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025

October 9, 2025
‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

‘Yansanda Sun Kama Motar Hilux Ɗin Da Aka Sace A Kano A Hanyar Zuwa Nijar

October 9, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

Sin Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Kawo Karshen Rikicin Gaza

October 9, 2025
TCN

Jami’an Tsaro Sun Cafke Ɓarayin Kayayyakin Turakun Wutar Lantarki Na Hanyar Mando Zuwa Jos

October 9, 2025
An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

An Yi Tafiye-tafiye Miliyan 16.34 Da Suka Shafi Shiga Da Fita Daga Kasar Sin Yayin Hutun Kwanaki 8 Na Kasar 

October 9, 2025
Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

Nijeriya Ta Yi Asarar Ganga Miliyan 13.5 Na Ɗanyen Mai Ta Hanyar Sata Da Zagon-ƙasa – NEITI

October 9, 2025
Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

Duniya Ta Kara Ganin Bunkasuwar Sin a Lokacin Hutun Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar

October 9, 2025
Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC

Batun Umarnin Kotu Na Kama Tsohon Shugaban INEC Ƙage Ne Kawai – Shugaban Jam’iyyar AA 

October 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.