• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron LEADERSHIP Da NDLEA Zai Gudana Ranar 7 Ga Nuwamba

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Taron LEADERSHIP Da NDLEA Zai Gudana Ranar 7 Ga Nuwamba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban taron LEADERSHIP tare da hadin gwiwar hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa (NDLEA) kan yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da aka daga zai gudana a ranar 7 ga watan Nuwamba.

A cikin wata sanarwa da LEADERSHIP ta fitar, kamfanin ya ce a yanzu za a gudanar da taron ne a ranar Talata 7 ga watan Nuwamba, 2023 a cibiyar ‘Yar’Adua da ke Abuja.

  • Tinubu Ya Kori Shugaban Hukumar NASENI Bayan Wata 3 Da Nadinsa
  • Yadda Sin Ta Kubuta Daga “Kangin Talauci”

Tun da farko dai an saka ranar 3 ga Agusta a matsayin ranar gudanar da taron, amma sakamakon wasu uzuri ya sa aka dage taron.

Sanarwar ta ce, “Muna matukar godiya da goyon baya da fahimtar abokan aikinmu da wadanda za su kashe kudadensu da kuma mahalarta taron, wadanda suka himmatu wajen samun nasarar wannan muhimmin babban taro da zai kawo mafita kan ta’ammuli da miyagun kwayoyi.

“Mun yi farin ciki da cewa daga karshe mun yanke ranar da za mu yi babban taron. An kuma inganta abubuwan da za su gudana a wurin taron sosai,” in ji sanarwar.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Taron mai taken, “Shaye-shayen miyagun kwayoyi, laifuka, rashin tsaro da ci gaban kasa,” abun yaba ne da shi a matsayin muhimmin matakin zamantakewa a wannan lokaci.

LEADERSHIP ta yi hadin gwiwa da hukumar NDLEA da abokan huldarta wadanda suka amince da daukar nauyin gudanar da babban taro domin bayyana illolin shaye-shayen miyagun kwayoyi da tasirinsa kan aikata laifuka da ci gaban kasa tare da yin nazari kan hanyoyin magance lamarin.

A binciken da Majalisar Dinkin Duniya ta yi na ta’ammuli da kwayoyi a shekarar 2017, bisa kiyasin al’ummar Nijeriya miliyan 98, ‘yan Nijeriya miliyan 14.3 ne ke ta’ammuli da miyagun kwayoyi da ke illata kwakwalwa.

Baya ga shugaban hukumar NDLEA, Buba Marwa, akwai mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu da kuma babban lauya mai fafutukar kare hakkin Bil’adama, Mista Femi Falana, da sauran su duk za su halarci babban taron.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kallo Ya Koma Sama: Greenwood Ya Koma Getafe

Next Post

An Cafke Mutum 23 Bisa Zargin Aikata Zamba Ta Intanet A Sakkwato

Related

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
Labarai

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

51 minutes ago
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)
Labarai

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

2 hours ago
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Labarai

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

3 hours ago
Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

15 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

16 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

18 hours ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

An Cafke Mutum 23 Bisa Zargin Aikata Zamba Ta Intanet A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

May 11, 2025
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

May 11, 2025
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

May 11, 2025
Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.