• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana ƙudirin Gwamnatin Tarayya na buɗe babbar makarantar koyar da aikin jarida da ilimin labarai ta Hukumar Ilimi, Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO Category 2 Institute for Media and Information Literacy) a Nijeriya ba tare da ɓata lokaci ba.

Ministan ya faɗi haka ne a wajen taron ƙasa da ƙasa na Mataimakin Darakta-Janar mai kula da Yaɗa Labarai na UNESCO, Dakta Tawfik Jelassi, a wani sashe na Babban Taro na 42 na hukumar UNESCO a ranar Talata a Paris, babban birnin ƙasar Faransa.

  • Rashin Tsaro: Za Mu Fara Horar Da Jami’an Sa-Kai Don Tsare Al’ummar Zamfara – Gwamna Lawal
  • Wadanne Damammaki Da Aka Samu Cikin Abubuwan Da Aka Nuna A Karon Farko A Duniya A CIIE?

Wannan alƙawari da Nijeriya ta yi na buɗe wa tare da ɗaukar nauyin makarantar, an yi shi ne tun lokacin da aka yi Makon Aikin Jarida da Yaɗa Labarai na Duniya na UNESCO na shekarar 2022, wanda aka yi a Nijeriya cikin Oktoba 2022, a Abuja, wanda kuma aka rattaba hannu kan ƙudirin aikin a Zama na 216 na Babbar Hukumar Gudanarwar UNESCO, cikin Mayu 2023.

Yayin da ya ke ƙara tabbatar da sadaukarwar Nijeriya ga manufofi da burukan UNESCO, Minista Idris ya bayyana cewa duk da yake ƙasar nan ta na shirin sauka daga kujerar ta a Majalisar Ƙasa da Ƙasa ta Shirin Cigaban Harkokin Yaɗa Labarai na Duniya na UNESCO (IPDC), bayan ta shafe shekaru shida a majalisar, to kuma ta na neman zama memba a Majalisar Ƙasa da Ƙasa ta Shirin Samar da Labarai ga Kowa, wato ‘Information for all Programme’ (IFAP).

 

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Idris ya sha alwashin cewa, zai tabbatar Nijeriya ta ci moriyar dukkan wasu damarmaki da ke akwai a Sashen Aikin Jarida da Yaɗa Labarai na UNESCO, ciki kuwa har da samar da ƙananan gidajen rediyo na unguwanni, wanda ya na daga cikin tsare-tsaren da UNESCO ta ke ba muhimmanci a yanzu.

Ministan ya kuma bayyana ƙudirinsa na dawo da darajar kafafen yaɗa labarai na gwamnatin Nijeriya, tare da kuma samar da tattaunawar ƙasa gaba ɗaya kan kyawawan ɗabi’u da halayen Nijeriya, a matsayin wani shirin gangamin wayar da kan jama’a da za a yi a duk faɗin ƙasar, wanda ya ce al’amari ne da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauka da muhimmanci.

Ministan ya gode wa Jakadiya Hajo Sani saboda aiki tuƙuru da ta ke yi na wakiltar burukan Nijeriya a UNESCO, da muhimmiyar rawar da ta taka wajen samar wa Nijeriya damar zama mai masaukin baƙi a Makon Aikin Jarida da Yaɗa Labarai na Duniya na UNESCO na shekarar 2022, da kuma shirye-shiryen da ake yi don ɗaukar nauyin da Nijeriya za ta yi na buɗe babbar makarantar ‘UNESCO MIL Institute’ ta farko a duk duniya.

Da ya ke mayar da jawabi, Mataimakin Darakta-Janar na UNESCO, Dakta Jelassi, ya yaba wa Nijeriya kan babbar rawar da ta ke takawa a UNESCO, sannan ya yi alƙawarin cewa, hukumar za ta ci gaba da mara wa ƙasar baya domin ta ci moriyar dukkan damarmakin da ke akwai na haɓaka ɓangarenta na aikin jarida da yaɗa labarai.

Ya lissafa ayyukan da UNESCO ke aiwatarwa a sassa daban-daban, daga tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida a ƙasashen duniya, zuwa tallafawa wajen kafa gidajen rediyo na unguwa, da aikin da ake yi don daidaita ayyukan da ƙasashe ke yi wajen yaƙar baza labaran bogi, da labaran ƙarya da kuma kalaman ɓatanci.

Tun da farko, mai girma Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya na cikin ayarin sauran mahalarta taron daga Nijeriya, ciki har da shugaban tafiyar, wato mai girma Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman (wanda kuma shi ne Shugaban Hukumar UNESCO ta Ƙasa), da su ka halarci bikin buɗe Babban Taro na 42 na UNESCO.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MDDMinistan yada labaraiUNESCO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ba Mu Janye Tsofaffin Takardun Naira Ba – CBN

Next Post

NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

8 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

10 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

11 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

11 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

13 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

15 hours ago
Next Post
NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.