• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taruka Biyu Na Sin Sun Bayyana Yadda Kasar Ke More Damar Ci Gaba Tare Da Kasashe Daban Daban

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

Ra’ayoyin da aka gabatar a taruka biyu na kasar Sin, wato taron majalisar wakilan jama’ar kasar (NPC), da na majalisar ba da shawarwari kan harkokin siyasa ta jama’ar kasar (CPPCC), ciki har da sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko, da neman ci gaba mai inganci, da zurfafa yin kwaskwarima da ma kara fadada bude kofa ga kasashen waje bisa wani matsayi mai karin inganci, wadanda suka jawo hankulan al’ummun kasashe daban daban. 

Wasu ‘yan kasashen waje sun bayyana cewa, tarukan biyu na kasar Sin sun nuna amincewar kasar ta fuskantar kalubale da sa kaimi wajen neman ci gaba, kana sun bayyana yadda kasar Sin ke more damar ci gaba tare da kasa da kasa, da ma yin aiki kafada da kafada tare da kasashen duniya.

  • Wakiliyar CPPCC Wadda Take Kokarin Neman Mafita Ga Sha’anin Kiwon Reindeer
  • Wakiliyar CPPCC Wadda Take Kokarin Neman Mafita Ga Sha’anin Kiwon Reindeer

Tsohon firaministan kasar Belgium Yves Leterme ya ce, ra’ayin raya sabon karfin samar da hajoji da hidimomi masu karko yana da kyau matuka, wadanda suka kasance babban ci gaba ne da kasar Sin ta samu a fannin tattalin arziki.

Wasu kuma sun bayyana cewa, ra’ayoyin ci gaba na kasar Sin sun jaddada muhimmancin raya kasa cikin lumana, da samun moriyar juna da kuma cimma nasara tare, suna kuma fatan kara gudanar da hadin gwiwa tare da kasar.

Tsohon ministan tattalin arziki da kudi na kasar Italiya Giovanni Tria ya ce, yana matukar kulawa da manufofin tattalin arzikin kasar Sin, kuma Sin za ta taka rawar gani a harkokin cinikayyar kasa da kasa, da bude kasuwanni, da samar da sauki ga mutanen kasashen waje wadanda ke neman zuba jari kan masana’antun kasar. A cewarsa, kasuwar kasar Sin na cike da damammaki ga jarin waje.

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

A nasa bangaren, tsohon firaministan kasar Iraki Adil Abdul-Mahdi ya bayyana cewa, ci gaban kasar Sin bai kwaikwayi tsarin wasu kasashe ba, haka kuma bai mamaye sararin ci gaba na sauran kasashe ba. Zamanintarwa irin ta kasar Sin na kokarta tabbatar da cigaba irin na samun moriya tare a zahiri. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Daga Birnin Sin

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Next Post
Tinubu Da IBB Sun Yi Ganawar Sirri A Neja

Tinubu Da IBB Sun Yi Ganawar Sirri A Neja

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Martani Kan Iƙirarin Trump Na Kisan Ƙare Dangi Ga Kiristoci

November 1, 2025
Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.