• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Bai Bude Iyakokin Nijeriya Ba -Kwastam

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Bai Bude Iyakokin Nijeriya Ba -Kwastam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar Hana Fasa Kauri ta Kasa (Kwastam) ta ce har yanzu shugaban kasa Bola Tinubu bai sake bude dukkan iyakokin kasar nan da tsohuwar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta rufe ba.

Idan za a tuna a shekarar 2019 ne, Buhari ya rufe dukkan iyakokin kasar nsn domin hana shigo da wasu kaya ba bisa ka’ida ba, wadanda suka hada da shinkafa, bindigogi da sauransu.

  • PSG Na Duba Yiwuwar Sayar Da Mbappe Kafin Kwantiraginsa Ya Kare
  • Batiya Wesley Na Shirin Zama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Adamawa

Bayan shekaru biyu, gwamnatin Buhari ta sake bude wasu kadan daga cikin iyakokin, wasu kuma sun kasance a rufe duk da kokawar da ‘yan Nijeriya suka yi.

A kwanakin baya ne wasu mutane suka fara yada wani tsohon faifan bidiyo a shafukan sada zumunta, inda aka ga Konturola na hukumar NCS reshen Ogun, Bamidele Makinde ya bude shingen da ke kan iyakar Idiroko da Jamhuriyar Benin.

An yada bidiyon tare da cewa Tinubu ya sake bude iyakokin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

Da yake mayar da martani, Konturola na NCS ya ce gwamnatin Tinubu ba ta ba da umarnin sake bude dukkan iyakokin kasar nan ba.

A cewarsa, gwamnatin Buhari a shekarar 2022 ta sake bude iyakar Idiroko da wasu ‘yan tsiraru, inda ya ce sauran na ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu karin umarni daga gwamnatin tarayya.

Bamidele ya bayyana cewa, sauran iyakokin da aka amince da su a jihar Ogun kamar Ijofin, Imeko, Ijoun da kuma Ohunbe na nan a kulle.

“Idiroko ne kawai aka bude yanzu; sauran kuma har yanzu a kulle suke,” in ji shi.

Makinde, yayin da yake zanta wa da manema labarai a Abeokuta, ya ci gaba da cewa jami’an Kwastam ma’aikatan gwamnati ne, wadanda aikinsu shi ne aiwatar da manufofin gwamnati.

“Yanzu, muna da sabuwar gwamnati. Sabuwar gwamnati za ta zo da manufofinta. Bai kamata a sami kuskure ba. Mu ma’aikatan gwamnati ne kawai, muna aiwatar da manufofi. Duk abin da Abuja ta ce muna yi,” a cewarsa.

Ya jaddada cewa, “Iyakar Idiroko na bude ko fa yaushe, amma a sauran idan muka kama mutum za mu kwace kayansa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariIyakokin NijeriyaKwastamShinkafaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hatsarin Mota Ya Yi Ajalin Kwamishinan Tarayya A Yobe

Next Post

Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

Related

‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

5 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

1 day ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

1 day ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

2 days ago
Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II
Manyan Labarai

Yawancin ‘Yan Siyasar Nijeriya Ba Su Da Tarbiyya – Sarki Sanusi II

2 days ago
Next Post
Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.