• English
  • Business News
Monday, October 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Bai Bude Iyakokin Nijeriya Ba -Kwastam

by Sadiq
2 years ago
Kwastam

Hukumar Hana Fasa Kauri ta Kasa (Kwastam) ta ce har yanzu shugaban kasa Bola Tinubu bai sake bude dukkan iyakokin kasar nan da tsohuwar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta rufe ba.

Idan za a tuna a shekarar 2019 ne, Buhari ya rufe dukkan iyakokin kasar nsn domin hana shigo da wasu kaya ba bisa ka’ida ba, wadanda suka hada da shinkafa, bindigogi da sauransu.

  • PSG Na Duba Yiwuwar Sayar Da Mbappe Kafin Kwantiraginsa Ya Kare
  • Batiya Wesley Na Shirin Zama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Adamawa

Bayan shekaru biyu, gwamnatin Buhari ta sake bude wasu kadan daga cikin iyakokin, wasu kuma sun kasance a rufe duk da kokawar da ‘yan Nijeriya suka yi.

A kwanakin baya ne wasu mutane suka fara yada wani tsohon faifan bidiyo a shafukan sada zumunta, inda aka ga Konturola na hukumar NCS reshen Ogun, Bamidele Makinde ya bude shingen da ke kan iyakar Idiroko da Jamhuriyar Benin.

An yada bidiyon tare da cewa Tinubu ya sake bude iyakokin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

Da yake mayar da martani, Konturola na NCS ya ce gwamnatin Tinubu ba ta ba da umarnin sake bude dukkan iyakokin kasar nan ba.

A cewarsa, gwamnatin Buhari a shekarar 2022 ta sake bude iyakar Idiroko da wasu ‘yan tsiraru, inda ya ce sauran na ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu karin umarni daga gwamnatin tarayya.

Bamidele ya bayyana cewa, sauran iyakokin da aka amince da su a jihar Ogun kamar Ijofin, Imeko, Ijoun da kuma Ohunbe na nan a kulle.

“Idiroko ne kawai aka bude yanzu; sauran kuma har yanzu a kulle suke,” in ji shi.

Makinde, yayin da yake zanta wa da manema labarai a Abeokuta, ya ci gaba da cewa jami’an Kwastam ma’aikatan gwamnati ne, wadanda aikinsu shi ne aiwatar da manufofin gwamnati.

“Yanzu, muna da sabuwar gwamnati. Sabuwar gwamnati za ta zo da manufofinta. Bai kamata a sami kuskure ba. Mu ma’aikatan gwamnati ne kawai, muna aiwatar da manufofi. Duk abin da Abuja ta ce muna yi,” a cewarsa.

Ya jaddada cewa, “Iyakar Idiroko na bude ko fa yaushe, amma a sauran idan muka kama mutum za mu kwace kayansa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba
Ilimi

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano
Manyan Labarai

Rundunar Ƴansanda Ta Kama Gaggan Ƴan Fashi 9 A Kano

October 13, 2025
nema
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya

October 13, 2025
Next Post
Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

Hukumar Kwastam Ta Tara Naira Biliyan ₦658.6 A Watan Satumba — DG Na NOA

October 13, 2025
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba

October 13, 2025
Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

Zargin Batanci: An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano

October 13, 2025
Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

Hada-Hadar Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 4% Cikin Watanni Tara Na Farkon Bana

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.