ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Bai Bude Iyakokin Nijeriya Ba -Kwastam

by Sadiq
3 years ago
Kwastam

Hukumar Hana Fasa Kauri ta Kasa (Kwastam) ta ce har yanzu shugaban kasa Bola Tinubu bai sake bude dukkan iyakokin kasar nan da tsohuwar gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta rufe ba.

Idan za a tuna a shekarar 2019 ne, Buhari ya rufe dukkan iyakokin kasar nsn domin hana shigo da wasu kaya ba bisa ka’ida ba, wadanda suka hada da shinkafa, bindigogi da sauransu.

  • PSG Na Duba Yiwuwar Sayar Da Mbappe Kafin Kwantiraginsa Ya Kare
  • Batiya Wesley Na Shirin Zama Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Adamawa

Bayan shekaru biyu, gwamnatin Buhari ta sake bude wasu kadan daga cikin iyakokin, wasu kuma sun kasance a rufe duk da kokawar da ‘yan Nijeriya suka yi.

ADVERTISEMENT

A kwanakin baya ne wasu mutane suka fara yada wani tsohon faifan bidiyo a shafukan sada zumunta, inda aka ga Konturola na hukumar NCS reshen Ogun, Bamidele Makinde ya bude shingen da ke kan iyakar Idiroko da Jamhuriyar Benin.

An yada bidiyon tare da cewa Tinubu ya sake bude iyakokin kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Da yake mayar da martani, Konturola na NCS ya ce gwamnatin Tinubu ba ta ba da umarnin sake bude dukkan iyakokin kasar nan ba.

A cewarsa, gwamnatin Buhari a shekarar 2022 ta sake bude iyakar Idiroko da wasu ‘yan tsiraru, inda ya ce sauran na ci gaba da kasancewa a rufe har sai an samu karin umarni daga gwamnatin tarayya.

Bamidele ya bayyana cewa, sauran iyakokin da aka amince da su a jihar Ogun kamar Ijofin, Imeko, Ijoun da kuma Ohunbe na nan a kulle.

“Idiroko ne kawai aka bude yanzu; sauran kuma har yanzu a kulle suke,” in ji shi.

Makinde, yayin da yake zanta wa da manema labarai a Abeokuta, ya ci gaba da cewa jami’an Kwastam ma’aikatan gwamnati ne, wadanda aikinsu shi ne aiwatar da manufofin gwamnati.

“Yanzu, muna da sabuwar gwamnati. Sabuwar gwamnati za ta zo da manufofinta. Bai kamata a sami kuskure ba. Mu ma’aikatan gwamnati ne kawai, muna aiwatar da manufofi. Duk abin da Abuja ta ce muna yi,” a cewarsa.

Ya jaddada cewa, “Iyakar Idiroko na bude ko fa yaushe, amma a sauran idan muka kama mutum za mu kwace kayansa.”

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

Sanata Akpabio Ya Lashe Zaben Shugaban Majalisar Dattawa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.