• English
  • Business News
Sunday, September 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Da Kwankwaso Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Dokta Idris Dutsen Tanshi

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Da Kwankwaso Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Dokta Idris Dutsen Tanshi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, sun bayyana alhininsu game da rasuwar fitaccen malamin addinin Musuluncin Jihar Bauchi, Dokta Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, wanda ya rasu yana da shekaru 68.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa , Bayo Onanuga, ya fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana Dokta Abdulaziz a matsayin ginshiƙi wajen koyar da tarbiyya da kyawawan ɗabi’u.

  • Tinubu Zai Yi Amfani Da Dokar Ta-ɓaci Wajen Tsoratar Da Gwamnoni Gabanin Zaben 2027 – Amaechi
  • APC Ta Musanta Zargin Sauya Kashim Shettima A Zaɓen 2027

“Dokta Abdulaziz ya kasance murya mai ƙarfi wajen kira zuwa gaskiya da ɗabi’u masu kyau.

“Ya tsaya tsayin daka wajen yaƙar tsattsauran ra’ayi, musamman a farkon fitowar Boko Haram, inda ya yi amfani da iliminsa da tasirinsa wajen wayar da kai da kawo zaman lafiya,” in ji Shugaba Tinubu.

Shugaban ya ƙara da cewa al’ummar Musulmi za su yi matuƙar kewar Dokta Abdulaziz saboda faɗakarwarsa da kira zuwa adalci da gaskiya.

Labarai Masu Nasaba

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

Ya roƙi Allah da Ya ji ƙansa, tare da bai wa iyalansa da almajiransa haƙurin rashinsa.

Hakazalika, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2023 kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana kaɗuwarsa game da fitaccen malamin.

Ya bayyana haka ne cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafukan sada zumunta.

“Ina miƙa ta’aziyya ta ga iyalai da almajiran Sheikh Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi.

“Dokts Dutsen Tanshi ya kasance abin tunawa saboda jajircewarsa wajen yaɗa ilimin addinin Musulunci.

“Allah Ya jikansa da rahama, Ya sanya shi a Aljannatul Firdausi,” in ji Kwankwaso.

Dokta Abdulaziz ya kasance mashahurin malami wanda aka san shi wajen faɗar gaskiya, kuma ya taka muhimmiyar rawa wajen yaƙi da tsattsauran ra’ayi da ƙarfafa zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin al’umma, musamman a Arewacin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BauchiDutsen TanshiKwankwasoMalamiRasuwarTa'aziyyaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Yi Amfani Da Dokar Ta-ɓaci Wajen Tsoratar Da Gwamnoni Gabanin Zaben 2027 – Amaechi

Next Post

Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Matakan Harajin Fito Na Amurka Sun Sa Ta Zama Makiyiyar Duniya

Related

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 
Manyan Labarai

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

3 hours ago
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Hallaka Mutane 61 A Jihar Borno

15 hours ago
Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutanen Gari Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Wasu A Sakkwato

19 hours ago
NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai
Manyan Labarai

NUPENG Za Ta Fara Yajin Aiki, Dangote Na Shirin Shiga Harkar Sufurin Mai

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

2 days ago
Sojoji Sun Kwato Makamai Da Babura, Sun Ceto Mutane 3 A Kaduna 
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ɗan Bindiga Ɗauke Da Makamai A Jihar Filato

2 days ago
Next Post
Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Matakan Harajin Fito Na Amurka Sun Sa Ta Zama Makiyiyar Duniya

Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Matakan Harajin Fito Na Amurka Sun Sa Ta Zama Makiyiyar Duniya

LABARAI MASU NASABA

ASUU

Malaman Jami’o’i Sun Zama Abin Tausayi —Kungiyar ASUU

September 7, 2025
Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

Gwamnati Ta Kaddamar Da Sabbin Darussan Karatu A Makarantun Nijeriya

September 7, 2025
Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

Zulum Ya Tabbatar Da Harin Boko Haram Ya Ci Rayukan Mutane 63 

September 7, 2025
Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

Mun Tara Kuɗi Sama Da Naira Miliyan 170 Na Fatun Layya – Sheikh Bala Lau 

September 7, 2025
Fyade

Matsalar Ciwon Kwakwalwa A Gidajen Yarin Kasar Nan

September 7, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Sake Maido Da Ma’aikatar Yaki A Amurka Ya Nuna Babu Dakatawa A Yaki Hatta A Wajen Sa Suna 

September 6, 2025
Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

Rikicin NNPP A Kano: Wani Tsagi Ya Soki Korar Abdulmumini Jibrin Kofa

September 6, 2025
Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

Koyo Daga Tarihi Da Kiyaye Zaman Lafiya Za Su Sa Kaimi Ga Zamanantar Da Duk Duniya Baki Daya

September 6, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

Neman Gurbin Kofin Duniya: Arokodare Ya Farfaɗo Da Mafarkin Nijeriya A Wasan Rwanda

September 6, 2025
Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

Babban Taron MDD Ya Zartas Da Kudurin Hadin Gwiwar MDD Da SCO

September 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.