• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu, Ka Taka Wa Wike Birki Ko Ka Fadi Warwas A Abuja A 2027 – Shugabannin APC

by Yusuf Shuaibu
1 year ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Babu Wani Shiri Na Kwaso ‘Yan Nijeriya Daga Falasdin Ko Isra’ila –Gwamnatin Tarayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugabannin APC a Abuja sun bayyana wa Shugaban kasa, Bola Tinubu cewa idan har bai taka wa ministan Abuja, Nyesom Wike birki ba, zai fadi warwas a zaben shugaban kasa na 2027, domin ko kuri’a da kashi 2 bisa 100 ba zai taba samu ba a yankin sakamakon yadda Wiken yake kashe jam’iyyar a Abuja. 

Haka kuma sun bayyana cewa lallai jam’iyyar za ta iya rasa zaben kananan hukumomi matukar aka kasa daukan mataki. Sun dai yi ikirarin cewa ministan na kashe siyasar jam’iyyar APC a Abuja sakamakon rashin ganin darajar jam’iyyar da shugabanninta.

  • An Fara Taron Kasa Da Kasa Kan Tsarin Dimokuradiyya Karo Na Uku A Nan Birnin Beijing
  • Ɗiawara Ya Fice Daga Tawagar Faransa Bayan An Hana ‘Yan Wasa Yin Azumi

Shugabannin jam’iyyar sun bayyana hakan ne a wani taron ‘yan jarida a Abuja, inda mambobin jam’iyyar suka koka kan nade-naden da Wike ya yi a ‘yan kwanakin nan.

Jiga-jigan shugabannin jam’iyyar karkashin jagorancin, Kwamared Abdulwahab Ekekhide da Dabid Omobolaji Obaje, sun ce tun lokacin da ministan ya kama aiki har zuwa yau bai taba zantawa da shugabannin jam’iyyar ba, duk da cewa jam’iyyar ta rubuta masa wasika na neman zantawa da shi, amma ya ki bayar da daman ganinsa.

Idan za a iya tunawa dai, Wike dan jam’iyyar PDP ne, amma Shugaba Tinubu ya nada shi ministan Abuja.

Labarai Masu Nasaba

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Ekekhide ya ce shugabannin da dukkan ‘ya’yan jam’iyyar APC a Abuja sun yi watsi da mukaman da ministan yake bayarwa, kuma suna ganin ministan yana hakan ne a matsayin cin mutuncin jam’iyyar APC a Abuja.

Ya ce, “Muna kira ga shugaban kasa wanda shi ne ya nada minista da ya ja masa kunne, saboda kauce wa rashin samun ko da kashi biyu na kuri’un da za a kada a zaben shugaba a 2027 da kuma zaben kananan hukumomi idan har ya kasa daukai kararen matakai.

“Kamar yadda muka sani, shugaban kasa yana sama da minista domin shi ne ya nada shi, kuma ya kasance wakilinsa, amma Wike yana cin dunduniyar shugaban kasa a kujeran ministan Abuja.

“Watannin baya da suka gabata, Wike ya  bayyana cewa babu wanda ya isa ya kashe masa siyasa a Jihar Ribas, amma kuma yanzu shi yana kashe siyasar shugaban kasa a Abuja.

“Dalilan da ya sa APC ta yake rashin nasara a Abuja a kowani zabe shi ne, ana nada ministoci wadanda ba su da wata akala siyasa a yankin gundumar Abuja, idan zabe ya zo sukan koma yankunan da suka fito su bar ganin Abuja, idan har ba a karfafa shugabanni da mambobin jam’iyyar ba ta yaya za a samu nasarar lashe zabe,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ku Yi Amanna Da Tinubu, Matsalolin Zu Su Zo Karshe, inji Ministan Yaɗa Labarai

Next Post

Sin Ta Raba Basira Da Karfinta Na Inganta Warware Rikicin Ukraine Ta Hanyar Siyasa

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 week ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 week ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 week ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2 weeks ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

2 weeks ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

3 weeks ago
Next Post
sin

Sin Ta Raba Basira Da Karfinta Na Inganta Warware Rikicin Ukraine Ta Hanyar Siyasa

LABARAI MASU NASABA

Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila

Son Zai Bar Tottenham Zuwa Amurka Bayan Shafe Shekaru 10 A Ingila

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.