• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

by Sadiq
2 months ago
in Manyan Labarai
0
Ganawar Tinubu Da Kwankwaso Alkairi Ce – Mataimakin Shugaban FUDMA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta ware Arewacin Najeriya wajen rabon albarkatun ƙasa.

Kwankwaso ya yi wannan magana ne a ranar Alhamis yayin wani taron tattaunawa da aka gudanar a Kano kan sauya tsarin kundin tsarin mulki.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

A cewarsa, gwamnatin tarayya na mayar da hankali kan ci gaban yankin Kudu, yayin da Arewa aka bar ta a baya.

Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai da Sadarwa, Sunday Dare, ya musanta kalaman Kwankwaso a shafinsa na X.

Ya ce ba a manta da Arewa ba, kuma Shugaba Tinubu na aiwatar da ayyuka a yankin.

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Dare, ya ce gwamnatin na gina manyan hanyoyi a Arewa kamar hanyar Abuja zuwa Kaduna, zuwa Zariya, har zuwa Kano, da hanyar Kano zuwa Maiduguri, da hanyar Sakkwato zuwa Badagry, da kuma wasu hanyoyi da suka haɗa jihohin Adamawa, Taraba, Kaduna da Jos.

A fannin lafiya, ya ce gwamnati na gyara da faɗaɗa wasu manyan asibitoci a Arewa kamar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Asibitin Koyarwa na Tarayya a Katsina, da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Ya kuma an gyara sama da cibiyoyin kiwon lafiya na guda 1,000 a yankin Arewa.

A fannin noma kuwa, Dare ya ce akwai wani shiri na Dala miliyan 158.15 da ake gudanarwa a jihohin Arewa tara domin bunƙasa harkar noma.

Haka ya ce, ana ci gaba da aikin wajen haƙo man fetur na Kolmani a Bauchi da Gombe, da aikin dam ɗin ruwa a Kano, da kuma shirin ACReSAL da Bankin Duniya ke ɗaukar nauyi domin farfaɗo da ƙasa da kuma kare muhalli a Arewa.

Ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka a sassan makamashi da sufuri, kamar bututun iskar gas daga Ajaokuta zuwa Kaduna har zuwa Kano mai tsawon kilomita 614, tashar wutar lantarki ta Gwagwalada da ke Abuja, da kuma tashar hasken rana da ake shirin ginawa a Kaduna.

Har ila yau, Dare ya kafa misalin inda ya ce an fara aikin layin dogo daga Kaduna zuwa Kano, daga Kano zuwa Maradi, da kuma aikin layin dogo na Kaduna wanda aka narka kuɗi Naira biliyan 100, tare da gyaran layin dogo na Abuja.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma bayyana wasu shirye-shiryen muhalli da kasuwanci kamar ayyukan Hukumar Great Green Wall da ke yaƙi da hamada a Arewa, da shirin NEWMAP da ke magance zaizayar ƙasa.

Sunday Dare ya ce duk waɗannan abubuwa an fara su ne cikin shekaru biyu kacal a ƙarƙashin shugabancin Tinubu, kuma hakan na nuna cewa ba a yi watsi da Arewa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArewaDareFadar Shugaban ƘasaKuduKwankwasoMartani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi

Next Post

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

8 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

9 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.