ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

by Sadiq
4 months ago
Kwankwaso

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta ware Arewacin Najeriya wajen rabon albarkatun ƙasa.

Kwankwaso ya yi wannan magana ne a ranar Alhamis yayin wani taron tattaunawa da aka gudanar a Kano kan sauya tsarin kundin tsarin mulki.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

A cewarsa, gwamnatin tarayya na mayar da hankali kan ci gaban yankin Kudu, yayin da Arewa aka bar ta a baya.

ADVERTISEMENT

Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai da Sadarwa, Sunday Dare, ya musanta kalaman Kwankwaso a shafinsa na X.

Ya ce ba a manta da Arewa ba, kuma Shugaba Tinubu na aiwatar da ayyuka a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Dare, ya ce gwamnatin na gina manyan hanyoyi a Arewa kamar hanyar Abuja zuwa Kaduna, zuwa Zariya, har zuwa Kano, da hanyar Kano zuwa Maiduguri, da hanyar Sakkwato zuwa Badagry, da kuma wasu hanyoyi da suka haɗa jihohin Adamawa, Taraba, Kaduna da Jos.

A fannin lafiya, ya ce gwamnati na gyara da faɗaɗa wasu manyan asibitoci a Arewa kamar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Asibitin Koyarwa na Tarayya a Katsina, da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Ya kuma an gyara sama da cibiyoyin kiwon lafiya na guda 1,000 a yankin Arewa.

A fannin noma kuwa, Dare ya ce akwai wani shiri na Dala miliyan 158.15 da ake gudanarwa a jihohin Arewa tara domin bunƙasa harkar noma.

Haka ya ce, ana ci gaba da aikin wajen haƙo man fetur na Kolmani a Bauchi da Gombe, da aikin dam ɗin ruwa a Kano, da kuma shirin ACReSAL da Bankin Duniya ke ɗaukar nauyi domin farfaɗo da ƙasa da kuma kare muhalli a Arewa.

Ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka a sassan makamashi da sufuri, kamar bututun iskar gas daga Ajaokuta zuwa Kaduna har zuwa Kano mai tsawon kilomita 614, tashar wutar lantarki ta Gwagwalada da ke Abuja, da kuma tashar hasken rana da ake shirin ginawa a Kaduna.

Har ila yau, Dare ya kafa misalin inda ya ce an fara aikin layin dogo daga Kaduna zuwa Kano, daga Kano zuwa Maradi, da kuma aikin layin dogo na Kaduna wanda aka narka kuɗi Naira biliyan 100, tare da gyaran layin dogo na Abuja.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma bayyana wasu shirye-shiryen muhalli da kasuwanci kamar ayyukan Hukumar Great Green Wall da ke yaƙi da hamada a Arewa, da shirin NEWMAP da ke magance zaizayar ƙasa.

Sunday Dare ya ce duk waɗannan abubuwa an fara su ne cikin shekaru biyu kacal a ƙarƙashin shugabancin Tinubu, kuma hakan na nuna cewa ba a yi watsi da Arewa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.