ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

by Sadiq
12 months ago
Kwankwaso

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta ware Arewacin Najeriya wajen rabon albarkatun ƙasa.

Kwankwaso ya yi wannan magana ne a ranar Alhamis yayin wani taron tattaunawa da aka gudanar a Kano kan sauya tsarin kundin tsarin mulki.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

A cewarsa, gwamnatin tarayya na mayar da hankali kan ci gaban yankin Kudu, yayin da Arewa aka bar ta a baya.

ADVERTISEMENT

Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai da Sadarwa, Sunday Dare, ya musanta kalaman Kwankwaso a shafinsa na X.

Ya ce ba a manta da Arewa ba, kuma Shugaba Tinubu na aiwatar da ayyuka a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

Dare, ya ce gwamnatin na gina manyan hanyoyi a Arewa kamar hanyar Abuja zuwa Kaduna, zuwa Zariya, har zuwa Kano, da hanyar Kano zuwa Maiduguri, da hanyar Sakkwato zuwa Badagry, da kuma wasu hanyoyi da suka haɗa jihohin Adamawa, Taraba, Kaduna da Jos.

A fannin lafiya, ya ce gwamnati na gyara da faɗaɗa wasu manyan asibitoci a Arewa kamar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Asibitin Koyarwa na Tarayya a Katsina, da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Ya kuma an gyara sama da cibiyoyin kiwon lafiya na guda 1,000 a yankin Arewa.

A fannin noma kuwa, Dare ya ce akwai wani shiri na Dala miliyan 158.15 da ake gudanarwa a jihohin Arewa tara domin bunƙasa harkar noma.

Haka ya ce, ana ci gaba da aikin wajen haƙo man fetur na Kolmani a Bauchi da Gombe, da aikin dam ɗin ruwa a Kano, da kuma shirin ACReSAL da Bankin Duniya ke ɗaukar nauyi domin farfaɗo da ƙasa da kuma kare muhalli a Arewa.

Ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka a sassan makamashi da sufuri, kamar bututun iskar gas daga Ajaokuta zuwa Kaduna har zuwa Kano mai tsawon kilomita 614, tashar wutar lantarki ta Gwagwalada da ke Abuja, da kuma tashar hasken rana da ake shirin ginawa a Kaduna.

Har ila yau, Dare ya kafa misalin inda ya ce an fara aikin layin dogo daga Kaduna zuwa Kano, daga Kano zuwa Maradi, da kuma aikin layin dogo na Kaduna wanda aka narka kuɗi Naira biliyan 100, tare da gyaran layin dogo na Abuja.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma bayyana wasu shirye-shiryen muhalli da kasuwanci kamar ayyukan Hukumar Great Green Wall da ke yaƙi da hamada a Arewa, da shirin NEWMAP da ke magance zaizayar ƙasa.

Sunday Dare ya ce duk waɗannan abubuwa an fara su ne cikin shekaru biyu kacal a ƙarƙashin shugabancin Tinubu, kuma hakan na nuna cewa ba a yi watsi da Arewa ba.

MASU ALAKA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.