ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Na Yi Wa Arewa Manyan Ayyuka – Martanin Fadar Shugaban Ƙasa Ga Kwankwaso 

by Sadiq
11 months ago
Kwankwaso

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta zargin da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta ware Arewacin Najeriya wajen rabon albarkatun ƙasa.

Kwankwaso ya yi wannan magana ne a ranar Alhamis yayin wani taron tattaunawa da aka gudanar a Kano kan sauya tsarin kundin tsarin mulki.

  • Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
  • Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato

A cewarsa, gwamnatin tarayya na mayar da hankali kan ci gaban yankin Kudu, yayin da Arewa aka bar ta a baya.

ADVERTISEMENT

Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai da Sadarwa, Sunday Dare, ya musanta kalaman Kwankwaso a shafinsa na X.

Ya ce ba a manta da Arewa ba, kuma Shugaba Tinubu na aiwatar da ayyuka a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

Dare, ya ce gwamnatin na gina manyan hanyoyi a Arewa kamar hanyar Abuja zuwa Kaduna, zuwa Zariya, har zuwa Kano, da hanyar Kano zuwa Maiduguri, da hanyar Sakkwato zuwa Badagry, da kuma wasu hanyoyi da suka haɗa jihohin Adamawa, Taraba, Kaduna da Jos.

A fannin lafiya, ya ce gwamnati na gyara da faɗaɗa wasu manyan asibitoci a Arewa kamar Asibitin Koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Asibitin Koyarwa na Tarayya a Katsina, da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

Ya kuma an gyara sama da cibiyoyin kiwon lafiya na guda 1,000 a yankin Arewa.

A fannin noma kuwa, Dare ya ce akwai wani shiri na Dala miliyan 158.15 da ake gudanarwa a jihohin Arewa tara domin bunƙasa harkar noma.

Haka ya ce, ana ci gaba da aikin wajen haƙo man fetur na Kolmani a Bauchi da Gombe, da aikin dam ɗin ruwa a Kano, da kuma shirin ACReSAL da Bankin Duniya ke ɗaukar nauyi domin farfaɗo da ƙasa da kuma kare muhalli a Arewa.

Ya ƙara da cewa akwai manyan ayyuka a sassan makamashi da sufuri, kamar bututun iskar gas daga Ajaokuta zuwa Kaduna har zuwa Kano mai tsawon kilomita 614, tashar wutar lantarki ta Gwagwalada da ke Abuja, da kuma tashar hasken rana da ake shirin ginawa a Kaduna.

Har ila yau, Dare ya kafa misalin inda ya ce an fara aikin layin dogo daga Kaduna zuwa Kano, daga Kano zuwa Maradi, da kuma aikin layin dogo na Kaduna wanda aka narka kuɗi Naira biliyan 100, tare da gyaran layin dogo na Abuja.

Fadar Shugaban Ƙasa ta kuma bayyana wasu shirye-shiryen muhalli da kasuwanci kamar ayyukan Hukumar Great Green Wall da ke yaƙi da hamada a Arewa, da shirin NEWMAP da ke magance zaizayar ƙasa.

Sunday Dare ya ce duk waɗannan abubuwa an fara su ne cikin shekaru biyu kacal a ƙarƙashin shugabancin Tinubu, kuma hakan na nuna cewa ba a yi watsi da Arewa ba.

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Tsaurara Tsaro A NIPSS Bayan Harin ’Yan Bindiga

June 19, 2026
INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6
Manyan Labarai

INEC Ta Kammala Shirye-shiryen Zaɓen Gwamnan Ekiti Da Zaɓukan Cike Gurbi A Jihohi 6

June 19, 2026
Next Post
Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Nemi Amurka Ta Maido Da Bizar Shekara Biyar Ga ‘Yan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Ƴan Bindiga Sun Tilasta Wa Ƙauyukan Sakkwato Biyan Sabon Haraji

June 20, 2026
IMF

Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

June 20, 2026
Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

Zulum Ya Ƙaddamar Da Gidajen Ƴan Gudun Hijira 100 A Sakkwato

June 20, 2026
Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.