• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci masu kada kuri’a a Jihar Yobe da kuma yankin Arewa Maso Gabashin kasar nan da su tabbatar da cewa sun zabi Bola Ahmed Tinubu a zabe mai zuwa.

Da yake jawabi a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a filin wasa na Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, shugaban kasar a wata sanarwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, ya ce zaben Tinubu da abokin takararsa, Kashim Shettima, ne kadai mafitar ‘yan Nijeriya.

  • Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 
  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Ya ce idan ana bukatar tabbatar da dorewar ci gaban da aka samu a fannin tsaro, tattalin arziki da ilimi a kasar nan dole a zabi dan takarar na APC.

Shugaban ya sha alwashin cewa bayan nasarar da aka samu a kan ‘yan ta’adda a yankin, gwamnatin APC ta yi kokarin karya lagon duk wanda ke barazana ga hadin kan Nijeriya.

Shugaban da yake jaddada bukatar ilimi wajen yakar akidar ta’addanci ta Boko Haram, ya shaida wa iyaye a Yobe cewa: “Ku tabbata kun tura ‘ya’yanku makaranta ku fahimtar da su cewa duk abin da kuke da shi a duniya za a iya kwace muku, ilimi ne kadai ba za a iya kwace muku ba.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

‘‘Ni maraya ne; ban san mahaifina ba. Na yi shekara tara a makarantar kwana kuma saboda ilimi aka kai ni aikin sojin Nijeriya.”

Ga masu rike da tutar jam’iyyar APC a zabe mai zuwa, shugaba Buhari ya kalubalanci su da su tabbatar da shugabanci na gari idan aka zabe su, ka da su bai wa jama’a kunya.

Ya bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta yi iya bakin kokarinta a cikin shekaru takwas da suka gabata a matakin tarayya kuma za ta ci gaba da tabbatar da ci gaba, wadata da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A nasa jawabin, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da karairayi da jam’iyyun adawa ke yi wa gwamnatin Buhari.

“Wannan gwamnati gwamnati ce ta ci gaba, rikon amana da gaskiya,” in ji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, wanda ya yaba wa Buhari kan samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Arewa maso Gabashin kasar nan, ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta mayar da yankin cibiyar sarrafa kayan gona ta Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaAPVBuhariMatsalar TsaroTinubuYakin Neman ZabeZaman Lafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 

Next Post

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Related

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

5 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

6 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

9 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

18 hours ago
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

23 hours ago
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

1 day ago
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma'aikata A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

September 18, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.