• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci masu kada kuri’a a Jihar Yobe da kuma yankin Arewa Maso Gabashin kasar nan da su tabbatar da cewa sun zabi Bola Ahmed Tinubu a zabe mai zuwa.

Da yake jawabi a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a filin wasa na Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, shugaban kasar a wata sanarwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, ya ce zaben Tinubu da abokin takararsa, Kashim Shettima, ne kadai mafitar ‘yan Nijeriya.

  • Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 
  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Ya ce idan ana bukatar tabbatar da dorewar ci gaban da aka samu a fannin tsaro, tattalin arziki da ilimi a kasar nan dole a zabi dan takarar na APC.

Shugaban ya sha alwashin cewa bayan nasarar da aka samu a kan ‘yan ta’adda a yankin, gwamnatin APC ta yi kokarin karya lagon duk wanda ke barazana ga hadin kan Nijeriya.

Shugaban da yake jaddada bukatar ilimi wajen yakar akidar ta’addanci ta Boko Haram, ya shaida wa iyaye a Yobe cewa: “Ku tabbata kun tura ‘ya’yanku makaranta ku fahimtar da su cewa duk abin da kuke da shi a duniya za a iya kwace muku, ilimi ne kadai ba za a iya kwace muku ba.

LABARAI MASU NASABA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

‘‘Ni maraya ne; ban san mahaifina ba. Na yi shekara tara a makarantar kwana kuma saboda ilimi aka kai ni aikin sojin Nijeriya.”

Ga masu rike da tutar jam’iyyar APC a zabe mai zuwa, shugaba Buhari ya kalubalanci su da su tabbatar da shugabanci na gari idan aka zabe su, ka da su bai wa jama’a kunya.

Ya bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta yi iya bakin kokarinta a cikin shekaru takwas da suka gabata a matakin tarayya kuma za ta ci gaba da tabbatar da ci gaba, wadata da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A nasa jawabin, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da karairayi da jam’iyyun adawa ke yi wa gwamnatin Buhari.

“Wannan gwamnati gwamnati ce ta ci gaba, rikon amana da gaskiya,” in ji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, wanda ya yaba wa Buhari kan samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Arewa maso Gabashin kasar nan, ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta mayar da yankin cibiyar sarrafa kayan gona ta Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Fursunoni: Saura Ƙasa Da Shekaru 6 Maryam Sanda Ta Shaƙi Iskar ‘Yanci

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Manyan Labarai

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa
Manyan Labarai

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma'aikata A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

Sakamakon Nazarin CGTN Ya Yabawa Gudunmuwar Sin Ga Dunkulewar Yankin Asiya Da Pasifik

October 29, 2025
Asuu

Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU

October 29, 2025
Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

Sabon Ingantaccen Hadin Gwiwar “Sin-ASEAN 3.0″ Ya Kafa Sabon Misali Na Hadin Kan Yanki

October 29, 2025
Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

Sulhu Da ’Yan Bindiga Ba Tare Da Sun Ajiye Makamai Ba Tamkar Miƙa Wuya Ne – Gwamna Lawal ga Hukumomin Tsaro

October 29, 2025
An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

An Yi Taron Tataunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Moscow, Manama, Da Budapest

October 29, 2025
majalisar kasa

Majalisar Wakilai Ta Amince Da Bukatar Amso Bashin Dala Biliyan 2.34 A Kasuwar Jari Ta Duniya

October 29, 2025
An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

An Samu Ingantuwar Yanayin Iska Da Ruwa Cikin Watanni 9 Na Farkon Bana A Sin

October 29, 2025
Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

Kotu Ta Umarci Ƙwace Dala 49,700 Daga Tsohon Jami’in INEC

October 29, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

Yadda Kasar Sin Ke Kara Kyautata Tsarin Kare Muradun Al’umma A Bangaren Shari’a

October 29, 2025
COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

COAS Shaibu Ya Sha Alwashin Murƙushe ‘Yan Ta’addar Lakurawa 

October 29, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.