ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 

by Sadiq
3 years ago
Birtaniya

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce ya samu kwarin guiwa sosai da irin kwazon da Birtaniya ke da shi na ganin Nijeriya ta farfado ta kowane fanni.

Atiku, ya bayyana hakan ne a shafinsa na Twitter, bayan ziyarar da ya kai Birtaniya domin ganawa da wasu jami’an gwamnatin.

  • Babu Gaskiya A Labarin Cewar G-5 Ta Goyi Bayan Takarar Atiku – Samuel Ortom
  • Buhari Ya Raka Tawagar Yakin Neman Zaben Tinubu Jihar Yobe

A ranar Litinin ne dan takarar na PDP ya tafi Birtaniya bisa gayyatar da gwamnatin kasar ta yi masa.

ADVERTISEMENT

A yayin ziyarar ta kwanaki biyu, Atiku zai tattauna da jami’an gwamnatin Birtaniya da kuma Archbishop na Canterbury, Justin Welby.

Atiku ya bayyana cewa ya gana da manyan jami’an gwamnatin Birtaniya da kuma Hon. Andrew Mitchell MP – Ministan Ci Gaban Afirka a Ofishin Harkokin Waje.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya kara da cewa ya bayyana musu hangen nesansa game da Nijeriya kamar yadda ya shirye sauya fasalin kasar nan.

“Na gana da Hon. Andrew Mitchell MP – Ministan Ci Gaban Afirka a Ofishin Harkokin Waje, tare da wasu manyan jami’an gwamnatin Birtaniya.

“Abin farin ciki ne na bayyana ra’ayina game da yadda ake son taimakon Nijeriya.

“Na nemi hadin gwiwarsu kuma na samu kwarin gwiwa daga irin kwazon da gwamnatin Birtaniya ke da shi na taimaka wa Nijeriya ta farfado a kowane fanni,” -AA.

Da yake karin haske kan muhimmancin ziyarar, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, ya kai Birtaniya, daraktan yada labaran kwamitin yakin neman zaben PDP, Dele Momodu, ya ce Birtaniya na da yakini mai kyau a kan Atiku shi ya sa ta gayyace shi.

Da farko dai an fara yada rade-radin cewar Atiku ya tafi Amurka ne sakamakon rashin lafiya da yake fama da ita.

Sai dai PDP ta musanta wannan zargi inda ta ce ya fice daga kasar nan ne sakamakon goron gayyata da aka aike masa.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.