ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ne Kadai Zai Iya Magance Rashin Tsaro Da Tabarbarewar Tattalin Arziki – Buhari 

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bukaci masu kada kuri’a a Jihar Yobe da kuma yankin Arewa Maso Gabashin kasar nan da su tabbatar da cewa sun zabi Bola Ahmed Tinubu a zabe mai zuwa.

Da yake jawabi a taron yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC a filin wasa na Damaturu, babban birnin Jihar Yobe, shugaban kasar a wata sanarwa ta hannun mai taimaka masa kan harkokin yada labarai, Femi Adesina, ya ce zaben Tinubu da abokin takararsa, Kashim Shettima, ne kadai mafitar ‘yan Nijeriya.

  • Birtaniya Na Son Taimaka Wa Nijeriya Ta Farfado – Atiku 
  • Aikin Hajjin 2023: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniyar Fahimtar Juna Da Gwamnatin Saudiyya

Ya ce idan ana bukatar tabbatar da dorewar ci gaban da aka samu a fannin tsaro, tattalin arziki da ilimi a kasar nan dole a zabi dan takarar na APC.

ADVERTISEMENT

Shugaban ya sha alwashin cewa bayan nasarar da aka samu a kan ‘yan ta’adda a yankin, gwamnatin APC ta yi kokarin karya lagon duk wanda ke barazana ga hadin kan Nijeriya.

Shugaban da yake jaddada bukatar ilimi wajen yakar akidar ta’addanci ta Boko Haram, ya shaida wa iyaye a Yobe cewa: “Ku tabbata kun tura ‘ya’yanku makaranta ku fahimtar da su cewa duk abin da kuke da shi a duniya za a iya kwace muku, ilimi ne kadai ba za a iya kwace muku ba.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

‘‘Ni maraya ne; ban san mahaifina ba. Na yi shekara tara a makarantar kwana kuma saboda ilimi aka kai ni aikin sojin Nijeriya.”

Ga masu rike da tutar jam’iyyar APC a zabe mai zuwa, shugaba Buhari ya kalubalanci su da su tabbatar da shugabanci na gari idan aka zabe su, ka da su bai wa jama’a kunya.

Ya bayyana cewa jam’iyyar mai mulki ta yi iya bakin kokarinta a cikin shekaru takwas da suka gabata a matakin tarayya kuma za ta ci gaba da tabbatar da ci gaba, wadata da kwanciyar hankali a Nijeriya.

A nasa jawabin, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da karairayi da jam’iyyun adawa ke yi wa gwamnatin Buhari.

“Wannan gwamnati gwamnati ce ta ci gaba, rikon amana da gaskiya,” in ji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, wanda ya yaba wa Buhari kan samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Arewa maso Gabashin kasar nan, ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta mayar da yankin cibiyar sarrafa kayan gona ta Nijeriya.

MASU ALAKA

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
Manyan Labarai

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta
Manyan Labarai

Kano Pillars Ta Naɗa Mataimakin Kocin Super Eagles, Daniel Ogunmodede A Matsayin Sabon Kocinta

July 3, 2026
Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Buƙaci EFCC, ICPC Su Sa Ido Kan Rabon Tallafin Taki

July 3, 2026
Next Post
Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma’aikata A Kaduna

Dan Takarar Gwamnan PDP Ya Nemi Goyon Bayan Ma'aikata A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.