ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Bukaci Ma’aikatu Su RIka Fitar Da Rahoton Kasafin Kudi Duk Wata

by Sadiq
3 years ago
TInubu

A wani  yunkuri na tabbatar da tsarin kasafin kudi mai inganci, Shugaba Bola Tinubu ya umarci dukkanin ma’aikatu da hukumomin gwamnati su rika fitar da rahoto duk wata kan yadda suka aiwatar da kasafin kudin 2024.

Da yake jawabi a wurin rattaba hannun a fadar shugaban kasa, a Abuja, Shugaba Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, gwamnatinsa za ta rinka bibiyar aiwatar da kasafin kudin na Naira tiriliyan 28.7 cikin tsanaki tare da sanya ido a kai.

  • Juyin Mulki: Faransa Ta Rufe Ofishin Jakadancinta Na Nijar
  • Zargin Sata: Jami’an ‘Yansanda A Kaduna Sun Kama Buhunan Taki Guda 600

Ya zayyana muhimman matakan da za a bi don tabbatar da bin ka’ida da inganci wajen aiwatar da kasafin kudin.

ADVERTISEMENT

“An umarci dukkanin hukumomi da ma’aikatun gwamnati su sani cewa, suna da nauyi da ya rataya a kansu na bayar da rahoton ayyukan kasafin kudi wata-wata ga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare ta tattalin arziki, wanda kuma zai tabbatar da sahihancin hakan,” in ji shugaba Tinubu.

Don kara inganta sa ido tabbatar da tabbatar da nasarar aikin, Shugaban kasar ya sanar da cewa, Ministan Kudi da na Tattalin Arziki za su rika yin bita akai-akai.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Kazalika, Shugaba Tinubu ya tabbatar da aniyarsa ta ganin nasarar tsarin ta hanyar jagorantar tarukan majalisar hadin kan tattalin arziki lokaci-lokaci.

Kasafin kudin shekarar 2024 mai taken ‘kasafin kudin sabunta fata’ ya ware kudade ga muhimman fannonin da za a fi ba da fifiko, da suka hada da tsaron cikin gida, samar da ayyukan yi, daidaita tattalin arzikin kasa, ingantaccen yanayin saka hannun jari, bunkasa jari, rage talauci, da samar da zaman lafiya.

Shugaban ya yi gargadi ga ma’aikatu da hukumomin gwamnati kan rahoton da ake bukata daga gare su.

“Ina so tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa, an gargadi dukkan hukumomi da ma’aikatunmu da cewa, idan ba za su iya aiwatatar da ayyukan gwamnati bisa inganci, sadaukarwa da amana ba, to lallai ya fi musu su tafi su bar aikinmu mu yi a madadin su.”

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Harbin Kasar Sin Ya Samu Bunkasuwar Yawon Shakatawa A Lokacin Hutun Murnar Sabuwar Shekara

Harbin Kasar Sin Ya Samu Bunkasuwar Yawon Shakatawa A Lokacin Hutun Murnar Sabuwar Shekara

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.