ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

by Sadiq
4 months ago
Tinubu

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce babu batun yin haɗin gwiwa tsakanin Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, kafin zaɓen 2027.

Yayin hira da gidan talabijin na Channels, Galadima ya zargi gwamnatin Tinubu da cin amanar Kwankwaso da NNPP a Kano, ta hanyar mara wa tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero, baya duk da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsige shi ta hanyar doka.

  • Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi
  • Dole Ne A Nace Kan Manufar Sin Daya Tak Don Kiyaye Zaman Lafiya A Mashigin Taiwan

“Ta yaya Kwankwaso zai yi abota da APC alhali suna yi mana haka a Kano? Sun kafa sarakuna biyu a gari guda; na Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin jiha. Wa ke da ikon naɗa Sarki da biyan albashinsa?” in ji Galadima.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na kare Aminy Ado Bayero ta hanyar samar masa da jami’an tsaro yayin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a wasu yankuna na Kano.

“Sun bai wa Sarkinsu (Aminu Ado Bayero) motocin ‘yansanda kusan 40 cike da jami’an Mopol, amma a wasu wurare a Kano ana kashe mutane, ana ƙwace musu wayoyi, amma ‘yansanda sun maƙale a waje ɗaya. Wannan ai abin kunya ne,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Galadima, ya tabbatar da cewa NNPP za ta taka muhimmiyar rawa wajen fitar da shugaban Nijeriya a 2027.

“Mu ne za mu yanke wanda zai zama shugaban ƙasa a 2027,” in ji shi, yana mai ƙaryata batun cewa Kwankwaso zai yi sulhu da Tinubu.

Ya ƙara da cewa: “Kar wani ya fito ya ce Kwankwaso zai shiga APC. Idan an nemi yin hakan zan sani. Kwankwaso ɗaya ne daga cikin manyan ‘yan siyasa a Nujeriya yanzu, ya ƙalubalanci APC a Kano ya kuma kayar da su.”

Rigimar sarautar Kano ta ƙara dagula siyasar jihar.

A shekarar 2014, Muhammadu Sanusi II ya zama Sarkin Kano bayan rasuwar marigayi Ado Bayero.

Amma a 2020, tsohon Gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya tsige shi, ya naɗa Aminu Ado Bayero.

A watan Mayun 2024, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sanusi II, lamarin da ya jawo Aminu Ado Bayero ya tafi kotu.

Tun daga wannan lokaci aka jibge jami’an tsaron tarayya a fadar da Aminu Ado Bayero ke zaune duk da cewa an tsige shi.

Galadima, ya ce Gwamnatin Tarayya na goyon bayan Bayero ne kawai saboda siyasa.

“Suna tunanin zai taimaka musu a 2027, amma babu wani Sarkin Kano da ya taɓa tantance wanda zai zama shugaban ƙasa,” in ji shi.

Jihar Kano ce ke da mafi yawan masu kaɗa ƙuri’a a Nijeriya.

A zaɓen 2023, ta kaɗa kusan ƙuri’u miliyan 1.7.

Kwankwaso ya fi kowa samu ƙuri’u, inda ya samu 997,279, Tinubu ya samu 517,341, Atiku Abubakar ya tashi da 131,716, yayin da Peter Obi ya samu 28,513.

Duk da cewa Kwankwaso ya zo na huɗu a zaɓen shugaban ƙasa da ƙuri’u miliyan 1.49, NNPP ta lashe zaɓe a ƙananan hukumomi 38 daga 44 a Kano, lamarin da ya nuna tasirinta a Arewa.

A halin yanzu, Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ne ke mulkin jihar, amma APC na riƙe da kujeru biyu daga cikin uku na Sanata a Kano, abin da ke nuna cewa za a kai ruwa rana a zaɓen 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.