ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

by Sadiq
3 months ago
Tinubu

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya ce babu batun yin haɗin gwiwa tsakanin Shugaba Bola Tinubu da tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, kafin zaɓen 2027.

Yayin hira da gidan talabijin na Channels, Galadima ya zargi gwamnatin Tinubu da cin amanar Kwankwaso da NNPP a Kano, ta hanyar mara wa tsohon Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero, baya duk da cewa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya tsige shi ta hanyar doka.

  • Manoma Na Neman Ɗauki Bayan Ambaliya Ta Lalata Gonakin Shinkafa A Kebbi
  • Dole Ne A Nace Kan Manufar Sin Daya Tak Don Kiyaye Zaman Lafiya A Mashigin Taiwan

“Ta yaya Kwankwaso zai yi abota da APC alhali suna yi mana haka a Kano? Sun kafa sarakuna biyu a gari guda; na Gwamnatin Tarayya da na Gwamnatin jiha. Wa ke da ikon naɗa Sarki da biyan albashinsa?” in ji Galadima.

ADVERTISEMENT

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na kare Aminy Ado Bayero ta hanyar samar masa da jami’an tsaro yayin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a wasu yankuna na Kano.

“Sun bai wa Sarkinsu (Aminu Ado Bayero) motocin ‘yansanda kusan 40 cike da jami’an Mopol, amma a wasu wurare a Kano ana kashe mutane, ana ƙwace musu wayoyi, amma ‘yansanda sun maƙale a waje ɗaya. Wannan ai abin kunya ne,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Galadima, ya tabbatar da cewa NNPP za ta taka muhimmiyar rawa wajen fitar da shugaban Nijeriya a 2027.

“Mu ne za mu yanke wanda zai zama shugaban ƙasa a 2027,” in ji shi, yana mai ƙaryata batun cewa Kwankwaso zai yi sulhu da Tinubu.

Ya ƙara da cewa: “Kar wani ya fito ya ce Kwankwaso zai shiga APC. Idan an nemi yin hakan zan sani. Kwankwaso ɗaya ne daga cikin manyan ‘yan siyasa a Nujeriya yanzu, ya ƙalubalanci APC a Kano ya kuma kayar da su.”

Rigimar sarautar Kano ta ƙara dagula siyasar jihar.

A shekarar 2014, Muhammadu Sanusi II ya zama Sarkin Kano bayan rasuwar marigayi Ado Bayero.

Amma a 2020, tsohon Gwamnan jihar Abdullahi Ganduje ya tsige shi, ya naɗa Aminu Ado Bayero.

A watan Mayun 2024, Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya dawo da Sanusi II, lamarin da ya jawo Aminu Ado Bayero ya tafi kotu.

Tun daga wannan lokaci aka jibge jami’an tsaron tarayya a fadar da Aminu Ado Bayero ke zaune duk da cewa an tsige shi.

Galadima, ya ce Gwamnatin Tarayya na goyon bayan Bayero ne kawai saboda siyasa.

“Suna tunanin zai taimaka musu a 2027, amma babu wani Sarkin Kano da ya taɓa tantance wanda zai zama shugaban ƙasa,” in ji shi.

Jihar Kano ce ke da mafi yawan masu kaɗa ƙuri’a a Nijeriya.

A zaɓen 2023, ta kaɗa kusan ƙuri’u miliyan 1.7.

Kwankwaso ya fi kowa samu ƙuri’u, inda ya samu 997,279, Tinubu ya samu 517,341, Atiku Abubakar ya tashi da 131,716, yayin da Peter Obi ya samu 28,513.

Duk da cewa Kwankwaso ya zo na huɗu a zaɓen shugaban ƙasa da ƙuri’u miliyan 1.49, NNPP ta lashe zaɓe a ƙananan hukumomi 38 daga 44 a Kano, lamarin da ya nuna tasirinta a Arewa.

A halin yanzu, Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ne ke mulkin jihar, amma APC na riƙe da kujeru biyu daga cikin uku na Sanata a Kano, abin da ke nuna cewa za a kai ruwa rana a zaɓen 2027.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

Akpabio Ya Ƙaryata Jita-jitar Ba Shi Da Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba 

November 17, 2025
Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.