ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Gana Da Tawagar Kamfanin Man Fetur Na Shell

by Sadiq
2 years ago
Tinubu

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya karbi bakuncin tawaga daga kamfanin raya man fetur na Shell a babban dakin taro na Aso Rock da ke Abuja.

Tawagar Shell a ziyarar ban girma karkashin jagorancin Daraktar kamfanin, Misis Zoe Yunovic tare da Peter Costello, Osagie Okunbo, da Mar De Jong.

  • Tinubu Ya Yi Ganawarsa Ta Farko Da Hafsoshin Tsaro
  • Hajjin Bana: Abin Da Ya Sa Alhazan Nijeriya 14 Suka Rasu

Babban jami’in rukunin kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPC), Mele Kyari; da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila su ma sun halarci taron.

ADVERTISEMENT

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan makamashi, Olu Verheijen; mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin kudaden shiga, Zacchaeus Adedeji; da kuma mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin sadarwa, ayyuka na musamman da dabaru, Dele Alake.

Taron na ranar Litinin ya biyo bayan komawar Tinubu Abuja a ranar Lahadi bayan da ya gudanar da bukukuwan Sallah a Legas a makon jiya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

A ranar 22 ga watan Yunin 2023 ne shugaban kasar ya yi ziyararsa ta farko zuwa kasashen waje bayan rantsar da shi a matsayin sabon shugaban Nijeriya a ranar 29 ga Mayu, 2023.

Tinubu ya je birnin Paris na kasar Faransa, tare da shugabannin duniya irin su shugaban kasar Faransa, Emmanuel Macron domin taron sabuwar yarjejeniyar hada-hadar kudi ta duniya da aka gudanar a Palais Brongniart.

Bayan kammala taron na kwanaki biyu, shugaban ya zarce zuwa birnin Landan na kasar Birtaniya domin yin wata ‘yar gajeriyar ziyarar sirri, sannan ya dawo Nijeriya domin gudanar da bukukuwan Sallah Babba a ranakun 28 da 29 ga watan Yunin 2023.

A zamansa na kwanaki biyar a Legas, Tinubu ya gana da sarakunan Yarbawa masu da suka hada da babban sarkin Ijebuland, Oba Sikiru Adetona; da Alake na Egbaland, Oba Adedotun Gbadebo, a Abeokuta, babban birnin jihar Ogun da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN
Labarai

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya
Labarai

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
Next Post
Matsalar Tsaro Kalubale Ne Ga Samar Da Abinci -Bafarawa

Matsalar Tsaro Kalubale Ne Ga Samar Da Abinci -Bafarawa

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025
Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

Shugaban Rasha Ya Bayyana Alakar Kasarsa Da Sin A Matsayin Matukar Muhimmanci Ga Samar Da Yanayin Daidaito A Duniya

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.