ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa, Ya Ce, Gwamnoni Ba Su Da Mafakar Bada Uzurin Gazawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya bukaci Gwamnonin Nijeriya da su yi aiki tukuru domin gudanar da shugabanci na kwarai ga al’ummar su.

Ya yi wannan bukatar ne a ranar Alhamis sa’ilin nan da ke kaddamar da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC), wanda mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ke jagoranta.

  • Siyasa Ta Wuce, Mu Hada Kai Don Ceto Jihar Mu, Gwamna Lawal Ya Roki Sabbin ‘Yan Majalisa

Dukkanin Gwamnonin Nijeriya su 36 tare da sauran Jami’ai ne suka kasance mambobin Majalisar.

ADVERTISEMENT

Tinubu ya ce, Gwamnoni ba su ma da uzurin da za su gabatar wajen kasa-kasau ko rashin nasara duk da roko, rokon a zabesu, har ma da rawar da suka taka domin a zabesu a lokacin yakin zaben 2023.

A cewarsa, ‘yan Nijeriya na bukatar a farfado da tattalin arziki cikin gaggawa, don haka akwai bukatar su hada hannu da Gwamnonin wajen cimma wannan nasarar.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Tinubu

Shugaban ya nemi Majalisar da ta hada karfi da karfe da gwamnatinsa domin cimma nasarori kan farfado da tattalin arzikin kasar nan cikin kankanin lokaci.

Bayan kaddamar da Majalisar, mambobin Majalisar sun shiga ganawa ta farko a fadar shugaban kasa da ke Villa, Abuja.

LEADERSHIP ta labarto cewa, NEC din na da alhakin bada shawarori wa shugaban kasa dangane da lamuran da suka shafi harkokin tattalin arzikin kasa da matakan da za a dauka wajen tsara hanyoyin da shirye-shiryen tafiyar da tattalin arziki na gwamnatoci da na tarayya.

Mambobin kwamitin sun hada da Gwamnonin Nijeriya su 36, gwamnan babban Bankin kasa (CBN) da kuma wasu jami’an gwamnati da aka shigo da su.

Tinubu

Daga cikin wadanda suka halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Kasa NEC a lokacin da aka fara sun hada Gwamnonin jihohin Kwara Abdulrahman Abdulrazaq; Osun, Ademola Adeleke; Kogi, Yahaya Bello; Ekiti, Biodun Oyebanji; Nasarawa, Abdullahi Sule; Akwa Ibom, Umo Eno, da kuma na jihar Enugu, Peter Mbah.

Sauran sun hada da Gwamnonin jihohin Cross River, Bassey Otu; Plateau, Caleb Mutfwang; Kebbi, Nasir Idris; Katsina, Umar Dikko Radda, da gwamnan Jihar Benue Hycinth Alia.

Kazalika a wajen ganawar akwai Gwamnonin Zamfara, Dauda Lawal; Ogun, Dapo Abiodun; Anambra, Charles Soludo; Yobe, Mai Mala Buni; Taraba, Agbu Kefas; Gombe State, Inuwa Yahaya; Delta, Sheriff Oborevwori; Rivers, Siminalayi Fubara; Niger, Mohammed Bago, da na jihar Sokoto, Ahmed Aliyu.

Saura sun hada da: Ebonyi, Francis Nwifuru; Kaduna, Uba Sani; Edo State, Godwin Obaseki; Abia, Alex Otti; Bayelsa, Douye Diri; Kano, Abba Yusuf; Bauchi, Bala Mohammed; Oyo, Seyi Makinde; da mai rikon mukamin gwamnan Jihar Ondo, Lucky Ayedatiwa, da kuma mataimakin Gwamnan Jihar Borno Borno, Umar Kadafur.

Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume; shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila; babban jami’in gudanarwa (GCEO) na kamfanin albarkatun Mai Mai kasa (NNPCL), Mele Kyari; mukaddashin Akanta-janar na tarayya, Oluwatoyin Madein; mukaddashin gwamnan CBN, Folashodun Shonubi; manyan sakatarorin ma’aikatar kasafi da tsare-tsaren tattalin arzikin, na birnin tarayya (FCTA) da na fadar shugaban kasa duk sun halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Nijeriya.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Harbe Mai Unguwa Har Lahira A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

MASU ALAKA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare
Labarai

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.