ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa, Ya Ce, Gwamnoni Ba Su Da Mafakar Bada Uzurin Gazawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya bukaci Gwamnonin Nijeriya da su yi aiki tukuru domin gudanar da shugabanci na kwarai ga al’ummar su.

Ya yi wannan bukatar ne a ranar Alhamis sa’ilin nan da ke kaddamar da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC), wanda mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ke jagoranta.

  • Siyasa Ta Wuce, Mu Hada Kai Don Ceto Jihar Mu, Gwamna Lawal Ya Roki Sabbin ‘Yan Majalisa

Dukkanin Gwamnonin Nijeriya su 36 tare da sauran Jami’ai ne suka kasance mambobin Majalisar.

ADVERTISEMENT

Tinubu ya ce, Gwamnoni ba su ma da uzurin da za su gabatar wajen kasa-kasau ko rashin nasara duk da roko, rokon a zabesu, har ma da rawar da suka taka domin a zabesu a lokacin yakin zaben 2023.

A cewarsa, ‘yan Nijeriya na bukatar a farfado da tattalin arziki cikin gaggawa, don haka akwai bukatar su hada hannu da Gwamnonin wajen cimma wannan nasarar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Tinubu

Shugaban ya nemi Majalisar da ta hada karfi da karfe da gwamnatinsa domin cimma nasarori kan farfado da tattalin arzikin kasar nan cikin kankanin lokaci.

Bayan kaddamar da Majalisar, mambobin Majalisar sun shiga ganawa ta farko a fadar shugaban kasa da ke Villa, Abuja.

LEADERSHIP ta labarto cewa, NEC din na da alhakin bada shawarori wa shugaban kasa dangane da lamuran da suka shafi harkokin tattalin arzikin kasa da matakan da za a dauka wajen tsara hanyoyin da shirye-shiryen tafiyar da tattalin arziki na gwamnatoci da na tarayya.

Mambobin kwamitin sun hada da Gwamnonin Nijeriya su 36, gwamnan babban Bankin kasa (CBN) da kuma wasu jami’an gwamnati da aka shigo da su.

Tinubu

Daga cikin wadanda suka halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Kasa NEC a lokacin da aka fara sun hada Gwamnonin jihohin Kwara Abdulrahman Abdulrazaq; Osun, Ademola Adeleke; Kogi, Yahaya Bello; Ekiti, Biodun Oyebanji; Nasarawa, Abdullahi Sule; Akwa Ibom, Umo Eno, da kuma na jihar Enugu, Peter Mbah.

Sauran sun hada da Gwamnonin jihohin Cross River, Bassey Otu; Plateau, Caleb Mutfwang; Kebbi, Nasir Idris; Katsina, Umar Dikko Radda, da gwamnan Jihar Benue Hycinth Alia.

Kazalika a wajen ganawar akwai Gwamnonin Zamfara, Dauda Lawal; Ogun, Dapo Abiodun; Anambra, Charles Soludo; Yobe, Mai Mala Buni; Taraba, Agbu Kefas; Gombe State, Inuwa Yahaya; Delta, Sheriff Oborevwori; Rivers, Siminalayi Fubara; Niger, Mohammed Bago, da na jihar Sokoto, Ahmed Aliyu.

Saura sun hada da: Ebonyi, Francis Nwifuru; Kaduna, Uba Sani; Edo State, Godwin Obaseki; Abia, Alex Otti; Bayelsa, Douye Diri; Kano, Abba Yusuf; Bauchi, Bala Mohammed; Oyo, Seyi Makinde; da mai rikon mukamin gwamnan Jihar Ondo, Lucky Ayedatiwa, da kuma mataimakin Gwamnan Jihar Borno Borno, Umar Kadafur.

Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume; shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila; babban jami’in gudanarwa (GCEO) na kamfanin albarkatun Mai Mai kasa (NNPCL), Mele Kyari; mukaddashin Akanta-janar na tarayya, Oluwatoyin Madein; mukaddashin gwamnan CBN, Folashodun Shonubi; manyan sakatarorin ma’aikatar kasafi da tsare-tsaren tattalin arzikin, na birnin tarayya (FCTA) da na fadar shugaban kasa duk sun halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Nijeriya.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ‘Yansanda Sun Cafke Tsoho Mai Shekara 70 Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 8 Fyaɗe A Bauchi

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.