ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa, Ya Ce, Gwamnoni Ba Su Da Mafakar Bada Uzurin Gazawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya bukaci Gwamnonin Nijeriya da su yi aiki tukuru domin gudanar da shugabanci na kwarai ga al’ummar su.

Ya yi wannan bukatar ne a ranar Alhamis sa’ilin nan da ke kaddamar da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC), wanda mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ke jagoranta.

  • Siyasa Ta Wuce, Mu Hada Kai Don Ceto Jihar Mu, Gwamna Lawal Ya Roki Sabbin ‘Yan Majalisa

Dukkanin Gwamnonin Nijeriya su 36 tare da sauran Jami’ai ne suka kasance mambobin Majalisar.

ADVERTISEMENT

Tinubu ya ce, Gwamnoni ba su ma da uzurin da za su gabatar wajen kasa-kasau ko rashin nasara duk da roko, rokon a zabesu, har ma da rawar da suka taka domin a zabesu a lokacin yakin zaben 2023.

A cewarsa, ‘yan Nijeriya na bukatar a farfado da tattalin arziki cikin gaggawa, don haka akwai bukatar su hada hannu da Gwamnonin wajen cimma wannan nasarar.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Tinubu

Shugaban ya nemi Majalisar da ta hada karfi da karfe da gwamnatinsa domin cimma nasarori kan farfado da tattalin arzikin kasar nan cikin kankanin lokaci.

Bayan kaddamar da Majalisar, mambobin Majalisar sun shiga ganawa ta farko a fadar shugaban kasa da ke Villa, Abuja.

LEADERSHIP ta labarto cewa, NEC din na da alhakin bada shawarori wa shugaban kasa dangane da lamuran da suka shafi harkokin tattalin arzikin kasa da matakan da za a dauka wajen tsara hanyoyin da shirye-shiryen tafiyar da tattalin arziki na gwamnatoci da na tarayya.

Mambobin kwamitin sun hada da Gwamnonin Nijeriya su 36, gwamnan babban Bankin kasa (CBN) da kuma wasu jami’an gwamnati da aka shigo da su.

Tinubu

Daga cikin wadanda suka halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Kasa NEC a lokacin da aka fara sun hada Gwamnonin jihohin Kwara Abdulrahman Abdulrazaq; Osun, Ademola Adeleke; Kogi, Yahaya Bello; Ekiti, Biodun Oyebanji; Nasarawa, Abdullahi Sule; Akwa Ibom, Umo Eno, da kuma na jihar Enugu, Peter Mbah.

Sauran sun hada da Gwamnonin jihohin Cross River, Bassey Otu; Plateau, Caleb Mutfwang; Kebbi, Nasir Idris; Katsina, Umar Dikko Radda, da gwamnan Jihar Benue Hycinth Alia.

Kazalika a wajen ganawar akwai Gwamnonin Zamfara, Dauda Lawal; Ogun, Dapo Abiodun; Anambra, Charles Soludo; Yobe, Mai Mala Buni; Taraba, Agbu Kefas; Gombe State, Inuwa Yahaya; Delta, Sheriff Oborevwori; Rivers, Siminalayi Fubara; Niger, Mohammed Bago, da na jihar Sokoto, Ahmed Aliyu.

Saura sun hada da: Ebonyi, Francis Nwifuru; Kaduna, Uba Sani; Edo State, Godwin Obaseki; Abia, Alex Otti; Bayelsa, Douye Diri; Kano, Abba Yusuf; Bauchi, Bala Mohammed; Oyo, Seyi Makinde; da mai rikon mukamin gwamnan Jihar Ondo, Lucky Ayedatiwa, da kuma mataimakin Gwamnan Jihar Borno Borno, Umar Kadafur.

Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume; shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila; babban jami’in gudanarwa (GCEO) na kamfanin albarkatun Mai Mai kasa (NNPCL), Mele Kyari; mukaddashin Akanta-janar na tarayya, Oluwatoyin Madein; mukaddashin gwamnan CBN, Folashodun Shonubi; manyan sakatarorin ma’aikatar kasafi da tsare-tsaren tattalin arzikin, na birnin tarayya (FCTA) da na fadar shugaban kasa duk sun halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Nijeriya.

Tinubu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.