• English
  • Business News
Thursday, July 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa, Ya Ce, Gwamnoni Ba Su Da Mafakar Bada Uzurin Gazawa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Kaddamar Da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa, Ya Ce, Gwamnoni Ba Su Da Mafakar Bada Uzurin Gazawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, ya bukaci Gwamnonin Nijeriya da su yi aiki tukuru domin gudanar da shugabanci na kwarai ga al’ummar su.

Ya yi wannan bukatar ne a ranar Alhamis sa’ilin nan da ke kaddamar da Majalisar Tattalin Arzikin Kasa (NEC), wanda mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ke jagoranta.

  • Siyasa Ta Wuce, Mu Hada Kai Don Ceto Jihar Mu, Gwamna Lawal Ya Roki Sabbin ‘Yan Majalisa

Dukkanin Gwamnonin Nijeriya su 36 tare da sauran Jami’ai ne suka kasance mambobin Majalisar.

Tinubu ya ce, Gwamnoni ba su ma da uzurin da za su gabatar wajen kasa-kasau ko rashin nasara duk da roko, rokon a zabesu, har ma da rawar da suka taka domin a zabesu a lokacin yakin zaben 2023.

A cewarsa, ‘yan Nijeriya na bukatar a farfado da tattalin arziki cikin gaggawa, don haka akwai bukatar su hada hannu da Gwamnonin wajen cimma wannan nasarar.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu

Shugaban ya nemi Majalisar da ta hada karfi da karfe da gwamnatinsa domin cimma nasarori kan farfado da tattalin arzikin kasar nan cikin kankanin lokaci.

Bayan kaddamar da Majalisar, mambobin Majalisar sun shiga ganawa ta farko a fadar shugaban kasa da ke Villa, Abuja.

LEADERSHIP ta labarto cewa, NEC din na da alhakin bada shawarori wa shugaban kasa dangane da lamuran da suka shafi harkokin tattalin arzikin kasa da matakan da za a dauka wajen tsara hanyoyin da shirye-shiryen tafiyar da tattalin arziki na gwamnatoci da na tarayya.

Mambobin kwamitin sun hada da Gwamnonin Nijeriya su 36, gwamnan babban Bankin kasa (CBN) da kuma wasu jami’an gwamnati da aka shigo da su.

Tinubu

Daga cikin wadanda suka halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Kasa NEC a lokacin da aka fara sun hada Gwamnonin jihohin Kwara Abdulrahman Abdulrazaq; Osun, Ademola Adeleke; Kogi, Yahaya Bello; Ekiti, Biodun Oyebanji; Nasarawa, Abdullahi Sule; Akwa Ibom, Umo Eno, da kuma na jihar Enugu, Peter Mbah.

Sauran sun hada da Gwamnonin jihohin Cross River, Bassey Otu; Plateau, Caleb Mutfwang; Kebbi, Nasir Idris; Katsina, Umar Dikko Radda, da gwamnan Jihar Benue Hycinth Alia.

Kazalika a wajen ganawar akwai Gwamnonin Zamfara, Dauda Lawal; Ogun, Dapo Abiodun; Anambra, Charles Soludo; Yobe, Mai Mala Buni; Taraba, Agbu Kefas; Gombe State, Inuwa Yahaya; Delta, Sheriff Oborevwori; Rivers, Siminalayi Fubara; Niger, Mohammed Bago, da na jihar Sokoto, Ahmed Aliyu.

Saura sun hada da: Ebonyi, Francis Nwifuru; Kaduna, Uba Sani; Edo State, Godwin Obaseki; Abia, Alex Otti; Bayelsa, Douye Diri; Kano, Abba Yusuf; Bauchi, Bala Mohammed; Oyo, Seyi Makinde; da mai rikon mukamin gwamnan Jihar Ondo, Lucky Ayedatiwa, da kuma mataimakin Gwamnan Jihar Borno Borno, Umar Kadafur.

Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume; shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Femi Gbajabiamila; babban jami’in gudanarwa (GCEO) na kamfanin albarkatun Mai Mai kasa (NNPCL), Mele Kyari; mukaddashin Akanta-janar na tarayya, Oluwatoyin Madein; mukaddashin gwamnan CBN, Folashodun Shonubi; manyan sakatarorin ma’aikatar kasafi da tsare-tsaren tattalin arzikin, na birnin tarayya (FCTA) da na fadar shugaban kasa duk sun halarci taron ganawar Majalisar Tattalin Arzikin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gayyaci Sirika Don Amsa Tambayoyi Kan Dodoridon Jirgin Nijeriya

Next Post

‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

Related

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

9 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

11 hours ago
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC
Labarai

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

12 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa JKS Mai Tsawon Tarihin Sama Da Shekaru 100 Ta Dore A Kan Mulki

13 hours ago
Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar HaÉ—aka
Manyan Labarai

Atiku, Obi, El-Rufai, Amaechi Da Wasu Sun Halarci Taron ADC Na jam’iyyar HaÉ—aka

14 hours ago
Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

17 hours ago
Next Post
‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Sake Kama Wani Tserarren Gidan Yarin Kuje A Jihar Nasarawa

LABARAI MASU NASABA

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi

July 2, 2025
Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

Gwamnatin Kano Ta Haramta Shigo Ƙarafu Daga Arewa maso Gabas

July 2, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar

July 2, 2025
Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya

July 2, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Cibiyar Fasahar Da Aka Lalata Lokacin Zanga-Zanga A Kano

July 2, 2025
Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma

July 2, 2025
Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

Abubakar Malami Ya Fice Daga APC, Ya Koma ADC

July 2, 2025
Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5

July 2, 2025
Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar

July 2, 2025
Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

Xi Ya Bukaci Kungiyoyin Matasa Da Dalibai Su Zurfafa Gyare-Gyare Da Kirkire-Kirkire Don Samun Sabbin Nasarori

July 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.