• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

by Abubakar Abba
3 weeks ago
in Noma Da Kiwo
0
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, ya kaddamar da babban sabon aikin noma na zamani da zummar kara samar da wadataccen abinci a Nijeriya.

Har ila yau, shirin ya kunshi rabar da kayan aikin noma na zamani daidai har guda 9,022, wadanda suka hada da Taraktocin noma, kayan Haro, kayan yin girbin amfanin gona da kuma sauran wasu kayan aikin noma.

  • APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

“Muna daukar kasar nan a matsayin daya daga cikin kasashen da suka mayar da hankali wajen aikin noma a fadin duniya, domin muna fitar da ingantaccen amfanin gona zuwa kasuwannin daban-daban a duniya tare kuma da tabbatar da kowane dan Nijeriya ya samu abinci mai gina jiki,” in ji Tinubu.

“Muna tunkaho da abin da muke ci gaba da yi, domin wannan kokarin na daga cikin alkawuranmu na yakin neman zabe da muke burin cika wa al’ummar wannan kasa.”

Tinubu ya ci gaba da cewa, gwamnatinsa ta dauki fannin aikin noma da matukar muhimmanci, domin fannni ne da ke samar da wadataccen abinci ga ‘yan kasa.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

“Wannan aiki ne, wanda za a iya cewa; tamkar a yanzu ne muka fara dora damba a kansa”, a cewar shugaban.

Haka zalika, shugaban ya kuma sanar da wadanda suka halaccin taron kaddamar da shirin tabbacin cewa; wadannan ayyuka na noman zamani, za su kara taimakawa wajen kara samar da ayyuka a fannin aikin noma sama da 2,000.

Ya ci gaba da cewa, kayan za su kuma taimaka wajen kara ayyukan masana’antun kasar da samar da damar gudanar da yin bita da kuma kwararrun kayan aikin noma 9,000.

Shugaban ya jaddada muhimmancin yin amfani da kayan aikin noma na zamani, wanda hakan zai taimaka wa manoman wannan kasa.

Har ila yau, ya kuma yi nuni da cewa; kaddamar da wannan shiri, wanda yake daidai na aikin noma a duniya, hakan zai kara bunkasa aikin noman kasar da samar da wadataccen abinci da kuma kara habaka tattalin arzikin Nijeriya.

“Ina so mu dauki wannan rana ta kaddamar da wannan shiri tamkar ranar farako ce da Nijeriya ta yunkuro, domin farfado da fannin aikin noman,“ in ji Tinubu.

“Yin noma da kayan aiki na zamani, shi ne kadai zai iya mayar da manoma tamkar wasu manyan jarumai,” a cewar shugaban.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, wannan shiri; an yi shi ne bisa hadaka da gwamnatin tarayya da kuma kamfanin da ke kera kayan aikin noma na zamani da aka fi sani da ‘APRE BNCC’.

Shi ma, babban Ministan Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari ya bayyana cewa; shirin ya kara tabbatar da yunkurin gwamnatin tarayya, wajen kara habaka fannin aikin noma na kasar, wanda kuma shi ne babban ginshikin ciyar da ta tattalin arzikin kasar gaba.

“Taron na yau da ka kaddamar, ba wai kawai shiri ne don mu ba, illa kawai wata manufa ce ta gwamnatin tarayya na cimma kudurin habaka fannin aikin noman kasar,“ in ji Kyari.

“Ana sa ran za a gudanar da shirin ne, a hekt sama da 550,000 tare da kuma da samar da sama da tan miliyan biyu na hatsi, inda kuma shirin zai samar da ayyukan yi sama da 16,000, wanda kuma sama da ‘yan cirani 560,000 da ke shiyoyi shida na kasar nan, za su amfana, a cewar Ministan.”

Kazalika, Kyari ya bayyana cewa; shirin ya kuma hada da samar da ingantattun Taraktocin noma 2,000, da kayan haro da na fanfunan ban ruwa masu feshi da kayan girbi da sauran makamantansu.

“Mun tanadi sama da na’urori masu kwakwalwa guda 9,000 da kuma kayan gyaransu guda 9,000,” in ji Ministan.

Shi kuwa, a nasa jawabin a wajen taron; Mataimakin Fira Ministan Jamhuriyar Belarus, Bictor Karankebich, ya nuna jin dadinsa kan wannan yarjejeniyar da Nijeriya ta kulla da kasarsa.

Ya bayyana cewa, Jamhuriyar ta Belarus, tana da dogon tarihi wajen kera kayan aikin noma, musamman duba da cewa; kasar ta tura kayan aikin noma da ta kera zuwa sama da kasashe 100 da ke fadin duniya.

Ya ce, shirin wanda ya kasance kashi na farko; ya jaddada muhimmancin bukatar kara hada guiwa, domin wanzar da kashi na biyu na shirin a kasar nan.

Ya ci gaba da cewa, kashin na wannan shiri, ya hada da samar da cibiyoyin hada Taraktocin noman da sauran kayan aikin noma da kuma bai wa manoma horo, domin sanin yadda za su sarrafa kayan aikin noman, wadanda akasarin kayan na zamani ne.

Idan za a iya tunawa, Majalisar Zartarwa ta Kasa a watan Agustan shekarar 2024 ne, ta amince da yarjejeniya a tsakanin Ma’aikatar Aikin Gona da Samar da Wadataccen Abinci da kuma Jamhuriyar ta Belarus.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Abinci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

Next Post

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Related

Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

7 days ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

7 days ago
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

3 weeks ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

4 weeks ago
Next Post
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau'ikan Dabbobi A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

July 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah

July 25, 2025
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.