Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya isa Jihar Benuwe a ranar Laraba sakamakon hare-haren da suka addabi al’ummar jihar, musamman a garin Yelwata da ke ƙaramar hukumar Guma.
Shugaban ya sauka a sansanin rundunar sojin sama da ke Makurdi da misalin ƙarfe 12:58 na rana.
- Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
- An ÆŠaure Wani Mutum Wata 6 Kan Satar Takalma A Masallaci A Kaduna
Ziyarar tasa na zuwa ne bayan fushin jama’a da jimamin ƙasa baki ɗaya saboda kisan da ya hallaka sama da mutum 100 cikin ‘yan makonnin da suka gabata.
A lokacin ziyarar, ana sa ran Tinubu zai je garin Yelwata tare da ganawa da sarakunan gargajiya, shugabannin ƙananan hukumomi da shugabannin tsaro.
Gwamnatin Jihar Benuwe ta ce tattaunawar za ta mayar da hankali kan yadda za a kawo ƙarshen matsalar tsaro a yankin.
Don girmama ziyarar shugaban ƙasa, gwamnatin jihar ta ayyana ranar Laraba a matsayin hutu domin bai wa mazauna yankunan damar halarta taron da kuma bin diddigin abubuwan da suka shafi ziyarar.
Wannan ita ce ziyarar farko da Tinubu ya kai Jihar Benuwe tun bayan da rikicin ya ƙara tsananta.
Jama’a da dama na kallon wannan ziyara a matsayin gwada gwamnati kan yadda za ta shawo kan matsalolin tsaro, musamman a jihohin da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga, rikicin makiyaya da na ƙabilanci.
Kisan da aka yi a Yelwata, wanda shi ne na baya-bayan nan cikin jerin hare-haren, ya janyo suka damuwa a faɗin ƙasar tare da ƙara matsin lamba ga shugaban ƙasa da ya ɗauki matakin gaggawa don tabbatar da adalci da tsaron rayukan jama’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp