Shugaba Bola Tinubu ya yi kira ga dukkan ‘yan Nijeriya da su shiga a yaƙi sha da fataucin miyagun ƙwayoyi, yana mai cewa ya kamata ya zama yaƙin kowa da kowa ba na gwamnati kadai ba.
Shugaban ya bayyana haka ne a bikin ranar yaƙi da miyagun ƙwayoyi na duniya da aka gudanar a babban zauren taro na fadar shugaban ƙasa a Abuja a ranar Alhamis.
“Wannan gwagwarmayar ba ta gwamnati kaɗai ba ce. Dole ne ta zama ta kowa da kowa – tun daga kan iyalai, shugabannin addini, ƙungiyoyin jama’a, matasa, da kuma waɗanda suka sha wahala daga miyagun ƙwayoyi,”
in ji Tinubu wanda SGF George Akume ya wakilta.
Shugaban ya kuma bayyana cewa yaƙin dole ne ya haɗa da magance talauci da rashin daidaito, yana mai cewa gwamnatinsu ta mayar da hankali ne kan wannan a matsayin wani ɓangare na shirin “Renewed Hope”.
A nasa ɓangaren, shugaban hukumar NDLEA, Brigadier-Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), ya ce Nijeriya tana cikin gaggawar ɗaukar matakan rigakafin shan miyagun ƙwayoyi.
“Ya kamata mu fahimci cewa batun shan ƙwayoyi ba a nesa yake ba – yana kusa da gidajenmu. Yara musamman suna cikin haɗarin koya” in ji Marwa.
Ya bayyana cewa NDLEA ta ƙara ƙarfafa matakan rigakafi yayin ci gaba da yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp