• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ce zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya wanda shi ne babban manufar gwamnatinsa.

Shugaban wanda ya karbi bakuncin kungiyar gwamnonin APC, karkashin jagorancin shugaban kungiyar, Gwamna Hope Uzodinma, na Jihar Imo, a fadar gwamnati, ya ce gwamnatocin kasa da na kananan hukumomi za su yi aiki tare a kan mafi karancin albashin ma’aikata, wanda tuni y fara aiki.

  • Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana
  • Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

“Muna bukatar yin wasu kididdiga da bincike a kan mafi karancin albashi.

“Dole ne mu kalli hakan tare, da kuma kudaden shiga. Dole ne mu karfafa tushe da kuma amfani da kudaden shigarmu, ”in ji shi.

A wata sanarwa da daraktan yada labarai, Abiodun Oladunjoye ya fitar, shugaba Tinubu ya bukaci gwamnonin da su yi amfani da damar da aka basu na zabar su a cikin miliyoyin al’ummar jihohinsu domin kawo sauyi a rayuwar jama’a, inda ya kara da cewa zai yi aiki da su domin amfanar da ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

“Wannan taron ba bakon abu bane a gare ni, kuma abubuwan da taron ya kunsa yana da matukar amfani. Wannan ya shafi aikin Nijeriya ne ba Bola Tinubu ba,’’ in ji shi.

Shugaban ya ce za a daidaita yawan kudaden musaya.

“Na gaji kadarori da kuma bashin wanda ya gabace ni. Wannan shi ne karon farko da muka shiga zauren majalisa, kuma wannan ne karo na farko da zan yi taro.

“A matsayinku na masu kawo ci gaba kuma masu tunani a karkashin inuwar jam’iyyar APC kuna da rawar da za ku taka wajen wayar da kan jama’armu da kuma tabbatar da cewa mun gudanar da aikinmu yadda ya kamata,” in ji shugaban.

Shugaba Tinubu ya ce wannan alama ce mai kyau da karfafa gwiwa cewa jam’iyyar APC na da rinjaye a Majalisar Dokoki ta kasa da wasu Majalisun dokoki, wanda hakan zai sa a samu sauki wajen samar da manufofin da za su shafi tattalin arziki da jama’a kai tsaye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Inganta AlbashiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Next Post

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Related

Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

12 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

13 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

15 hours ago
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama
Labarai

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

16 hours ago
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don Yaƙi Da Ta’addanci

18 hours ago
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
Labarai

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

19 hours ago
Next Post
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.