ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Yi Alkawarin Inganta Mafi Karancin Albashin Ma’aikata

by Sadiq
3 years ago
Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ce zai inganta rayuwar ‘yan Nijeriya wanda shi ne babban manufar gwamnatinsa.

Shugaban wanda ya karbi bakuncin kungiyar gwamnonin APC, karkashin jagorancin shugaban kungiyar, Gwamna Hope Uzodinma, na Jihar Imo, a fadar gwamnati, ya ce gwamnatocin kasa da na kananan hukumomi za su yi aiki tare a kan mafi karancin albashin ma’aikata, wanda tuni y fara aiki.

  • Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana
  • Kungiyar Kwadago Za Ta Shiga Yajin Aiki Kan Cire Tallafin Man Fetur

“Muna bukatar yin wasu kididdiga da bincike a kan mafi karancin albashi.

ADVERTISEMENT

“Dole ne mu kalli hakan tare, da kuma kudaden shiga. Dole ne mu karfafa tushe da kuma amfani da kudaden shigarmu, ”in ji shi.

A wata sanarwa da daraktan yada labarai, Abiodun Oladunjoye ya fitar, shugaba Tinubu ya bukaci gwamnonin da su yi amfani da damar da aka basu na zabar su a cikin miliyoyin al’ummar jihohinsu domin kawo sauyi a rayuwar jama’a, inda ya kara da cewa zai yi aiki da su domin amfanar da ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

“Wannan taron ba bakon abu bane a gare ni, kuma abubuwan da taron ya kunsa yana da matukar amfani. Wannan ya shafi aikin Nijeriya ne ba Bola Tinubu ba,’’ in ji shi.

Shugaban ya ce za a daidaita yawan kudaden musaya.

“Na gaji kadarori da kuma bashin wanda ya gabace ni. Wannan shi ne karon farko da muka shiga zauren majalisa, kuma wannan ne karo na farko da zan yi taro.

“A matsayinku na masu kawo ci gaba kuma masu tunani a karkashin inuwar jam’iyyar APC kuna da rawar da za ku taka wajen wayar da kan jama’armu da kuma tabbatar da cewa mun gudanar da aikinmu yadda ya kamata,” in ji shugaban.

Shugaba Tinubu ya ce wannan alama ce mai kyau da karfafa gwiwa cewa jam’iyyar APC na da rinjaye a Majalisar Dokoki ta kasa da wasu Majalisun dokoki, wanda hakan zai sa a samu sauki wajen samar da manufofin da za su shafi tattalin arziki da jama’a kai tsaye.

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

Shawarwarin Tsohon Shugaban Kasa Babangida Ga Tinubu

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.