• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

An sake gurfanar da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a gaban kotun koli bisa zarginsa da gabatar da kansa a matsayin shugaban kasa ba bisa ka’ida ba, lokacin da ake jiran hukuncin kotu kan gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.

Dan takarar shugaban kasa a zaben 2019, Cif Albert Ambrose Owuru ne ya shigar da wannan kara, inda ya bukaci kotun kolin ta soke bikin rantsar da Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa a 2023.

  • Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba
  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD

Owuru wanda ya kasance lauyan, ya ce zaben shugaban kasa da ya bayyana nasarar Tinubu, ba ya bisa ka’ida.

Karamar kotun koli mai lamba SC/667/2023, ta bayyana cewa Owuru da jam’iyyarsa ta HDP sun daukaka kara ne a yayin da wadanda ake tuhuma sun hada da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, AGF, INEC, da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Owuru yana kalubanci ayyana Tinubu a matsayin shugaban kasa da INEC ta yi a matsayin cin fuska ne ga kotun koli da kuma dokar da aka kafa. Ya kara da cewa tun da Tinubu yana cikin bangaren da ake kara a gaban kotun koli, bai kamata ya gabatar da kansa ba a matsayin shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

Shi dai Owuru ya tsaya takarar shugaban kasa a 2019 karkashin tutar jam’iyyar HDP, wanda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya yi ikirarin shi ne ya lashe zaben ba Buhari ba da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ayyana ba.

Tsohon dan takarar shugaban kasa ya bukaci kotun koli da ta hana Tinubu yin amfani da asusun tarayya har sai an kammala shari’ar da ke gaban kotu na zaben zaben 2023.

Owuru wanda ya yi ikirarin cewa shi ne wanda tsarin mulki ya tabbatar da ya lashe zaben shugaban kasa na 2019, kuma bai kamata a rantsar da wani a matsayin magajin Buhari ba har sai ya kammala wa’adinsa na shiekara hudu kamar yadda doka ta tanada.

Owuru ya dage cewa Buhari ne ya kwace masa mulki a 2019, saboda kotun koli ba ta tantance karar da ya shigar a 2019 ba, inda ya kalubalanci ayyana Buhari a matsayin wanda ya lashe zaben.

Mai shari’a Inyang Edem Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ne ya yi watsi da kararsa ta farko a ranar 30 ga watan Janairun 2023, lamarin da ya sa ya koma kotun daukaka kara.

Kotun daukaka kara da ke Abuja a nata bangaren, ranar 25 ga watan Mayu a hukuncin da mai shari’a Jamil Tukur wanda ya jagoranci alkalan kutun mutum uku ya ki dakatar da bikin rantsar da Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

peter
Tambarin Dimokuradiyya

Peter Obi Ya Bukaci INEC Ta Tabbatar Da Shaidar Karatun Dan Takara Kafin Shiga Zabe

October 10, 2025
Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Maƙiyan Jonathan Ne Kaɗai Za Su Zuga Shi Ya Fito Takara A 2027 – Oshiomhole

October 10, 2025
Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya
Tambarin Dimokuradiyya

Majalisa Na Duba Yiwuwar Amincewa Da Gudanar Da Zaɓen 2027 A Rana Ɗaya

October 10, 2025
Next Post
TGI

TGI Group Za Ta Hada Kai Da ABU Domin Bunkasa Kirkire-kirkire

LABARAI MASU NASABA

Kotu

Kotu A Kano Ta Tsare Wani Mai Gidan Marayu Bisa Zargin Satar Yara Da Safararsu Zuwa Delta

October 14, 2025
Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.