• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An sake gurfanar da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a gaban kotun koli bisa zarginsa da gabatar da kansa a matsayin shugaban kasa ba bisa ka’ida ba, lokacin da ake jiran hukuncin kotu kan gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.

Dan takarar shugaban kasa a zaben 2019, Cif Albert Ambrose Owuru ne ya shigar da wannan kara, inda ya bukaci kotun kolin ta soke bikin rantsar da Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa a 2023.

  • Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba
  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD

Owuru wanda ya kasance lauyan, ya ce zaben shugaban kasa da ya bayyana nasarar Tinubu, ba ya bisa ka’ida.

Karamar kotun koli mai lamba SC/667/2023, ta bayyana cewa Owuru da jam’iyyarsa ta HDP sun daukaka kara ne a yayin da wadanda ake tuhuma sun hada da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, AGF, INEC, da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Owuru yana kalubanci ayyana Tinubu a matsayin shugaban kasa da INEC ta yi a matsayin cin fuska ne ga kotun koli da kuma dokar da aka kafa. Ya kara da cewa tun da Tinubu yana cikin bangaren da ake kara a gaban kotun koli, bai kamata ya gabatar da kansa ba a matsayin shugaban kasa.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Shi dai Owuru ya tsaya takarar shugaban kasa a 2019 karkashin tutar jam’iyyar HDP, wanda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya yi ikirarin shi ne ya lashe zaben ba Buhari ba da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ayyana ba.

Tsohon dan takarar shugaban kasa ya bukaci kotun koli da ta hana Tinubu yin amfani da asusun tarayya har sai an kammala shari’ar da ke gaban kotu na zaben zaben 2023.

Owuru wanda ya yi ikirarin cewa shi ne wanda tsarin mulki ya tabbatar da ya lashe zaben shugaban kasa na 2019, kuma bai kamata a rantsar da wani a matsayin magajin Buhari ba har sai ya kammala wa’adinsa na shiekara hudu kamar yadda doka ta tanada.

Owuru ya dage cewa Buhari ne ya kwace masa mulki a 2019, saboda kotun koli ba ta tantance karar da ya shigar a 2019 ba, inda ya kalubalanci ayyana Buhari a matsayin wanda ya lashe zaben.

Mai shari’a Inyang Edem Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ne ya yi watsi da kararsa ta farko a ranar 30 ga watan Janairun 2023, lamarin da ya sa ya koma kotun daukaka kara.

Kotun daukaka kara da ke Abuja a nata bangaren, ranar 25 ga watan Mayu a hukuncin da mai shari’a Jamil Tukur wanda ya jagoranci alkalan kutun mutum uku ya ki dakatar da bikin rantsar da Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun KoliKotun sauraron kararrakin zabeSiyasaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Za Ta Zaftare Kudaden Kananan Hukumomin Da Ba A Yi Zabe Ba

Next Post

TGI Group Za Ta Hada Kai Da ABU Domin Bunkasa Kirkire-kirkire

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

24 hours ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 day ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 day ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
TGI

TGI Group Za Ta Hada Kai Da ABU Domin Bunkasa Kirkire-kirkire

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.