ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Zai Sake Fuskantar Wata Shari’ar A Kotun Koli Kan Zaben 2023

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

An sake gurfanar da Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a gaban kotun koli bisa zarginsa da gabatar da kansa a matsayin shugaban kasa ba bisa ka’ida ba, lokacin da ake jiran hukuncin kotu kan gudanar da zaben shugaban kasa na 2023.

Dan takarar shugaban kasa a zaben 2019, Cif Albert Ambrose Owuru ne ya shigar da wannan kara, inda ya bukaci kotun kolin ta soke bikin rantsar da Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa a 2023.

  • Hukumar Kwastam A Kano Ta Samu Kudin Shiga Naira Biliyan 6.9 A Nuwamba
  • Za A Shiga Mummunar Damuwa A Gaza Idan Ba Ku Dauki Mataki Ba – Gargadi Ga Majalisar Tsaro Ta MDD

Owuru wanda ya kasance lauyan, ya ce zaben shugaban kasa da ya bayyana nasarar Tinubu, ba ya bisa ka’ida.

ADVERTISEMENT

Karamar kotun koli mai lamba SC/667/2023, ta bayyana cewa Owuru da jam’iyyarsa ta HDP sun daukaka kara ne a yayin da wadanda ake tuhuma sun hada da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, AGF, INEC, da Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Owuru yana kalubanci ayyana Tinubu a matsayin shugaban kasa da INEC ta yi a matsayin cin fuska ne ga kotun koli da kuma dokar da aka kafa. Ya kara da cewa tun da Tinubu yana cikin bangaren da ake kara a gaban kotun koli, bai kamata ya gabatar da kansa ba a matsayin shugaban kasa.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Shi dai Owuru ya tsaya takarar shugaban kasa a 2019 karkashin tutar jam’iyyar HDP, wanda ya sha kaye a hannun tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, inda ya yi ikirarin shi ne ya lashe zaben ba Buhari ba da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta ayyana ba.

Tsohon dan takarar shugaban kasa ya bukaci kotun koli da ta hana Tinubu yin amfani da asusun tarayya har sai an kammala shari’ar da ke gaban kotu na zaben zaben 2023.

Owuru wanda ya yi ikirarin cewa shi ne wanda tsarin mulki ya tabbatar da ya lashe zaben shugaban kasa na 2019, kuma bai kamata a rantsar da wani a matsayin magajin Buhari ba har sai ya kammala wa’adinsa na shiekara hudu kamar yadda doka ta tanada.

Owuru ya dage cewa Buhari ne ya kwace masa mulki a 2019, saboda kotun koli ba ta tantance karar da ya shigar a 2019 ba, inda ya kalubalanci ayyana Buhari a matsayin wanda ya lashe zaben.

Mai shari’a Inyang Edem Ekwo na babbar kotun tarayya da ke Abuja ne ya yi watsi da kararsa ta farko a ranar 30 ga watan Janairun 2023, lamarin da ya sa ya koma kotun daukaka kara.

Kotun daukaka kara da ke Abuja a nata bangaren, ranar 25 ga watan Mayu a hukuncin da mai shari’a Jamil Tukur wanda ya jagoranci alkalan kutun mutum uku ya ki dakatar da bikin rantsar da Tinubu a ranar 29 ga watan Mayu.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
TGI

TGI Group Za Ta Hada Kai Da ABU Domin Bunkasa Kirkire-kirkire

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.