ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa Ba Zai Sa Tinubu Ya Yi Murabus Ba: Martanin Gwamnatin Tarayya Ga Gwamnonin PDP 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Gwamnatin tarayya ta yi zazzafar martani ga gwamnonin jam’iyyar PDP, inda ta bayyana cewa Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ba zai yi murabus  daga shugabancin Nijeriya ba sakamakon tsadar rayuwa da ake ciki.

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ba zai yi murabus ba saboda halin da tattalin arziki ke ciki.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Ministan ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Rabiu Ibrahim, ya fitar lokacin da yake mayar da martani ga gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP kan kiran shugaban kasa ya yi murabus saboda tsadar rayuwa da ke fama da ita a kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cawarsa, kiran da gwamnonin jam’iyyar adawan ke yi ba wani abu ba ne illa fusata mutane wadanda suke biyayya ga shugaban kasa wajen kokarinsa na kawo sauki ga al’ummar Nijeriya.

Ya ce jam’iyyar PDP da gwamnoninta bai kamata su biyo ta bayan fage wajen sukar gwamnati ba, domin sun gaza cimma irin wannan kokarin lokacin da suke rike da jan ragamar shugabancin Nijeriya har zuwa 2015.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“Wadanda suka kasa kawo sauyi lokacin da suke da dama, bai kamata su dunga janye hankalin mutane wajen sukar shugaban da ke da muradin kawo sauyi da ‘yan Nijeriya suka zaba ba.

“Tun farkon wannan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bayar da kudade ga gwamnatocin jihoji ba tare da nuna wani bambancin jam’iyyar ba. Bugu da kari, cire tallafin man fetur yana daga cikin manyan abubuwan da dan takarar shugaban kasa na PDP ya ayyana a lokacin yakin neman zabe a matsayin wata hanyar da zai samar wa dukkan jihohi kudaden shiga. Saboda haka wannan ba abun suka ba ne,” in ji Idris.

Idris ya ce shugaban kasa yana aiki tukuru wajen farfado da tattalin arziki ta hanyar wasu shirye-shirye da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya fara na inganta ababen more rayuwa, tallafa wa al’umma, samar da kayayyakin aiki da kulawa da jin dadin jami’an tsaro da kuma sake dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Ya nanata cewa ‘yan Nijeriya ba za su taba mantawa da gwamnatin APC ba, saboda ita ce ta biya wasu basuka da gwamnatin PDP ta ciyo domin biyan kudin tallafi da kasa biyan kudaden fansho da albashin ma’aikata.

Ya kuma ce an gyara manyan bangarori na man fetur da PDP ta gaza gyarawa shekaru da dama tare da gina sabbin matatan mai da kuma sauran ayyukan ci gaba da APC take shimfidawa a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : “Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina” 

Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : "Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina" 

LABARAI MASU NASABA

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025
NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

NIQS Ta Buƙaci Gwamnati Ta Tsawatar Kan Tsadar Gidajen Haya A Manyan Birane

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.