• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa Ba Zai Sa Tinubu Ya Yi Murabus Ba: Martanin Gwamnatin Tarayya Ga Gwamnonin PDP 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta yi zazzafar martani ga gwamnonin jam’iyyar PDP, inda ta bayyana cewa Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ba zai yi murabus  daga shugabancin Nijeriya ba sakamakon tsadar rayuwa da ake ciki.

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ba zai yi murabus ba saboda halin da tattalin arziki ke ciki.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Ministan ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Rabiu Ibrahim, ya fitar lokacin da yake mayar da martani ga gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP kan kiran shugaban kasa ya yi murabus saboda tsadar rayuwa da ke fama da ita a kasar nan.

A cawarsa, kiran da gwamnonin jam’iyyar adawan ke yi ba wani abu ba ne illa fusata mutane wadanda suke biyayya ga shugaban kasa wajen kokarinsa na kawo sauki ga al’ummar Nijeriya.

Ya ce jam’iyyar PDP da gwamnoninta bai kamata su biyo ta bayan fage wajen sukar gwamnati ba, domin sun gaza cimma irin wannan kokarin lokacin da suke rike da jan ragamar shugabancin Nijeriya har zuwa 2015.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

“Wadanda suka kasa kawo sauyi lokacin da suke da dama, bai kamata su dunga janye hankalin mutane wajen sukar shugaban da ke da muradin kawo sauyi da ‘yan Nijeriya suka zaba ba.

“Tun farkon wannan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bayar da kudade ga gwamnatocin jihoji ba tare da nuna wani bambancin jam’iyyar ba. Bugu da kari, cire tallafin man fetur yana daga cikin manyan abubuwan da dan takarar shugaban kasa na PDP ya ayyana a lokacin yakin neman zabe a matsayin wata hanyar da zai samar wa dukkan jihohi kudaden shiga. Saboda haka wannan ba abun suka ba ne,” in ji Idris.

Idris ya ce shugaban kasa yana aiki tukuru wajen farfado da tattalin arziki ta hanyar wasu shirye-shirye da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya fara na inganta ababen more rayuwa, tallafa wa al’umma, samar da kayayyakin aiki da kulawa da jin dadin jami’an tsaro da kuma sake dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Ya nanata cewa ‘yan Nijeriya ba za su taba mantawa da gwamnatin APC ba, saboda ita ce ta biya wasu basuka da gwamnatin PDP ta ciyo domin biyan kudin tallafi da kasa biyan kudaden fansho da albashin ma’aikata.

Ya kuma ce an gyara manyan bangarori na man fetur da PDP ta gaza gyarawa shekaru da dama tare da gina sabbin matatan mai da kuma sauran ayyukan ci gaba da APC take shimfidawa a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Babban Jami’in JKS Ya Bukaci A Himmantu Wajen Ciyar Da Kokarin Dunkulewar Kasar Gaba 

Next Post

Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : “Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina” 

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : “Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina” 

Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : "Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina" 

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.