ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa Ba Zai Sa Tinubu Ya Yi Murabus Ba: Martanin Gwamnatin Tarayya Ga Gwamnonin PDP 

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tinubu

Gwamnatin tarayya ta yi zazzafar martani ga gwamnonin jam’iyyar PDP, inda ta bayyana cewa Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ba zai yi murabus  daga shugabancin Nijeriya ba sakamakon tsadar rayuwa da ake ciki.

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ba zai yi murabus ba saboda halin da tattalin arziki ke ciki.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Ministan ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Rabiu Ibrahim, ya fitar lokacin da yake mayar da martani ga gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP kan kiran shugaban kasa ya yi murabus saboda tsadar rayuwa da ke fama da ita a kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cawarsa, kiran da gwamnonin jam’iyyar adawan ke yi ba wani abu ba ne illa fusata mutane wadanda suke biyayya ga shugaban kasa wajen kokarinsa na kawo sauki ga al’ummar Nijeriya.

Ya ce jam’iyyar PDP da gwamnoninta bai kamata su biyo ta bayan fage wajen sukar gwamnati ba, domin sun gaza cimma irin wannan kokarin lokacin da suke rike da jan ragamar shugabancin Nijeriya har zuwa 2015.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

“Wadanda suka kasa kawo sauyi lokacin da suke da dama, bai kamata su dunga janye hankalin mutane wajen sukar shugaban da ke da muradin kawo sauyi da ‘yan Nijeriya suka zaba ba.

“Tun farkon wannan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bayar da kudade ga gwamnatocin jihoji ba tare da nuna wani bambancin jam’iyyar ba. Bugu da kari, cire tallafin man fetur yana daga cikin manyan abubuwan da dan takarar shugaban kasa na PDP ya ayyana a lokacin yakin neman zabe a matsayin wata hanyar da zai samar wa dukkan jihohi kudaden shiga. Saboda haka wannan ba abun suka ba ne,” in ji Idris.

Idris ya ce shugaban kasa yana aiki tukuru wajen farfado da tattalin arziki ta hanyar wasu shirye-shirye da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya fara na inganta ababen more rayuwa, tallafa wa al’umma, samar da kayayyakin aiki da kulawa da jin dadin jami’an tsaro da kuma sake dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Ya nanata cewa ‘yan Nijeriya ba za su taba mantawa da gwamnatin APC ba, saboda ita ce ta biya wasu basuka da gwamnatin PDP ta ciyo domin biyan kudin tallafi da kasa biyan kudaden fansho da albashin ma’aikata.

Ya kuma ce an gyara manyan bangarori na man fetur da PDP ta gaza gyarawa shekaru da dama tare da gina sabbin matatan mai da kuma sauran ayyukan ci gaba da APC take shimfidawa a Nijeriya.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : “Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina” 

Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : "Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina" 

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.