ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Rayuwa Ba Zai Sa Tinubu Ya Yi Murabus Ba: Martanin Gwamnatin Tarayya Ga Gwamnonin PDP 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Tinubu

Gwamnatin tarayya ta yi zazzafar martani ga gwamnonin jam’iyyar PDP, inda ta bayyana cewa Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ba zai yi murabus  daga shugabancin Nijeriya ba sakamakon tsadar rayuwa da ake ciki.

Ministan yada labarai, Mohammed Idris, ya jaddada cewa Shugaba Tinubu ba zai yi murabus ba saboda halin da tattalin arziki ke ciki.

  • ‘Yan Nijeriya Ku Ba Wa Tinubu Ƙarin Lokaci Zai Magance Matsalolin Nijeriya – Gowon
  • Gwamnatin Kaduna Ta Tabbatar Da Kashe Jagoran ‘Yan Ta’adda Boderi

Ministan ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Rabiu Ibrahim, ya fitar lokacin da yake mayar da martani ga gwamnonin jam’iyyar adawa ta PDP kan kiran shugaban kasa ya yi murabus saboda tsadar rayuwa da ke fama da ita a kasar nan.

ADVERTISEMENT

A cawarsa, kiran da gwamnonin jam’iyyar adawan ke yi ba wani abu ba ne illa fusata mutane wadanda suke biyayya ga shugaban kasa wajen kokarinsa na kawo sauki ga al’ummar Nijeriya.

Ya ce jam’iyyar PDP da gwamnoninta bai kamata su biyo ta bayan fage wajen sukar gwamnati ba, domin sun gaza cimma irin wannan kokarin lokacin da suke rike da jan ragamar shugabancin Nijeriya har zuwa 2015.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

“Wadanda suka kasa kawo sauyi lokacin da suke da dama, bai kamata su dunga janye hankalin mutane wajen sukar shugaban da ke da muradin kawo sauyi da ‘yan Nijeriya suka zaba ba.

“Tun farkon wannan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta bayar da kudade ga gwamnatocin jihoji ba tare da nuna wani bambancin jam’iyyar ba. Bugu da kari, cire tallafin man fetur yana daga cikin manyan abubuwan da dan takarar shugaban kasa na PDP ya ayyana a lokacin yakin neman zabe a matsayin wata hanyar da zai samar wa dukkan jihohi kudaden shiga. Saboda haka wannan ba abun suka ba ne,” in ji Idris.

Idris ya ce shugaban kasa yana aiki tukuru wajen farfado da tattalin arziki ta hanyar wasu shirye-shirye da tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya fara na inganta ababen more rayuwa, tallafa wa al’umma, samar da kayayyakin aiki da kulawa da jin dadin jami’an tsaro da kuma sake dawo da Nijeriya cikin hayyacinta.

Ya nanata cewa ‘yan Nijeriya ba za su taba mantawa da gwamnatin APC ba, saboda ita ce ta biya wasu basuka da gwamnatin PDP ta ciyo domin biyan kudin tallafi da kasa biyan kudaden fansho da albashin ma’aikata.

Ya kuma ce an gyara manyan bangarori na man fetur da PDP ta gaza gyarawa shekaru da dama tare da gina sabbin matatan mai da kuma sauran ayyukan ci gaba da APC take shimfidawa a Nijeriya.

Tinubu
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : “Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina” 

Gwamnatin Tarayya Ga Masu Shagon Magunguna Da Aka Rufe A Kano : "Ku Koma Sabuwar Cibiyar Da Aka Gina" 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.