• English
  • Business News
Sunday, May 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar ‘Yan Tsaki Da Abincinsu Na Neman Tilasta  Dakatar Da Sana’ar

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsadar ‘Yan Tsaki Da Abincinsu Na Neman Tilasta  Dakatar Da Sana’ar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yayin da Nijeriya ke ci gaba da fusknatar kalubalen tattalin arziki da kuma hauhawan farashin kaya wanda wasu ke ganin, shi ne ma fi tsananai a cikin shekara 17 da suka wuce, hakan ya kuma shafi masu sana’ar kiwata Kajin gidan gona, inda wasu masu sana’ar a jihar kasno wadanda tsadar ‘yan tsakin da abincinsu, ta tilasata su dakatar da sana’ar.

Wani mai yin sana’ar a jihar Bala Idris ya bayyana cewa, wasu daga cikin masu sanar’ar a jihar ta Kano sun durkushe saboda wannan matsalar, inda wasu da daman masu sana’ar ke ta fafutura neman mafita, saboda irin wannan kalubalen da fannin ke fuskanta a jihar.

  • Adabin Zamanin Da Na Sin (3)
  • Ana Baje Kolin Shirye-Shiryen CMG A Taron Kafofin Watsa Labaran Kasa Da Kasa Karo Na Farko

Wasu masu sana’ar sun ce, farashin na abincin Kaji da kuma farashin ‘yan tsakin ya fi tashi a cikin watan Nuwamba zuwa Disamba, amma a bana,tashin farashin ya yi kamari matuka.

Wasu masu ruwa da tsaki a fannin da ke jihar Yakubu Ibrahim, wanada ke da gonar kiwon Kajin da ake kira ‘Albarka’ ya  bayyana cewa, saboda wadannan kalubalen a yanzu, ba ya iyan sana’ar kamar da, inda ya kara da cewa, a da, ba su taba fuskantar wannan kalubalen ba.

Ibrahim ya ce, akwai abubuwa da dama da suka jawo haka, wadanda suka hada da tsadar Kajin da abincinsu, inda hakan ya jawo masu sana’ar ke fice daga cikinta.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Ya kara da cewa, ana kuma fuskantar kalubalen masu yin kyankyasar ‘yan tsakin a jihar, inda ya kara da cewa, daukacin ‘yan tsakin ana shigo da su ne daga kudancin kasar nan domin akasari ba a cika samun kamfanonin da ke yin kyankyasar ‘yan tsakin a jihar ba.

Ibrahim ya ce, masu kiwon Kaji da ake kira da ‘Broilers’ a Ingilishi, su ne suka fi fuskantar wannan kalubalen domin farashinsu ya tashi matuka wanda kuma ba a taba ganin hakan ba.

A cewarsa, a baya hakan ya fi aukuwa a lokacin bukukuwan karshen shekara lokacin gudanar da bikin Kirismeti, domin masu kiwata su na ci gaba da kiwon su ne har tsawon wata uku ko hudu.

“Masu kiwon Kaji da ake kira ‘Broilers’ a jihar, su ne suka fi fuskantar wannan kalubalen domin farashin su ya tashi matuka wanda kuma ba a taba ganin hakan a ba yaba”.

Bincike ya nuna cewa, a yanzu haka ana kara samun bukatar Kajin, inda hakan ya kuma shafi rabar da Kajin a yankin Arewa.

A yanzu dai, ana sayar da ‘yan tsakin kyankyasar kwana daya akan naira 800, inda kuma ba a iya sayen ‘yan tsakin da aka kyankyashe a cikin  sati biyu ganin cewa, ko wanne daya ana sayar wa akan naira 1,000 kuma babu wanda zai yarda ya sayi ko wanne daya  akan naira 2,000.

Shi ma wani da ke wannan sana’a mai suna Mansur Shehu Kiru da ke da gonar Kajin da ake kira da Rahama Agro ya bayyana cewa, ya rage yawan Kajin  daga 2,000 zuwa 400  saboda tsadar safarar su daga garin Ibadan zuwa  Kano.

Ya ci gaba da cewa, magunguna Kajin ma sun yi tashin gwaron zabi, inda ya kara da cewa,  wannan ma bababn kalubale ne da masu sana’ar ke fusktana a jihar.

Ya ce, a ‘yan tsakin na broiler a shekarar da ta wuce, ana sayar duk kwara daya ta ‘yan tsakin su akan naira 500 amma yanzu farashin ya kai daga naira 800 zuwa naira  850.

Mansur Shehu a baya ana sayar da buhun  abincin ‘yan tsaki ne akan naira 3,500 , amma a yanzu farshin ya kai daga 8,000 zuwa naira  9,000.

Shi ma wani mai ruwa da tsaki a fannin Zaharaddin Yakasai wanda keda gonar kiwon da ake kira da Yaks a jihar Kano, ya sanar da cewa, abincin Kajin ya yi matukar tsada a bana, musamman saboda mastin tattalin arziki da kasar nan ke fuskanta.

Zaharaddin Yakasai ya bayyana cewa, saboda wadannan kalubalen wasu masu sana’ra sun dakatar, domin tafiyar da fannin a yanzu, akwai matukar wahala.

 Ya sanar da cewa, idan ka lissafa zaka ga ba wata ribar kirki muke samu ba, inda ya ce, wasu na barin sana;ar wasu kuma sun rage yawan adadin wadanda suka kiwata wa.

A cewar Zaharaddin Yakasai, akwai matukar bukara gwamnati ta kawo mana dauki, musamman ganin yadda fannin ke taimaka wa wajen samar da ayyukan yin a kai tsaye da kuma wadanda ba ana kai tsaye ba a jihar, musamman a tsakanin matasan da ke a jihar

Zaharaddin Yakasai ya kuma koka akan yadda duk da  wadanna kalubalen da masu sana’ar a fannin ke ci gaba da fuskanta, amma masu karbar haraji tin daga na kananan hukomomi har zuwa matkin jiha ba sa daga masu kafa, inda ya sanar da cewa, masu karbar harajin na karbar daga naiora 100,000 zuwa naira 300,000.

“Akwai matukar bukara gwamnati ta kawo mana dauki, musamman ganin yadda fannin ke taimaka wa wajen samar da ayyukan yi na kai tsaye da kuma wadanda ba na kai tsaye ba a jihar, musamman a tsakanin matasan da ke a jihar”.

Shi ma wani dilan ‘yan tsaki da sauran tsintsaye a jihar Abdurrahman Suleiman Tarauni ya bayyana cewa, sana’ar yanzu ba ta tafiya yadda ya kamata, inda ya kara da cewa, a yanzu ana sayar da abincin Kajin daga naira 8,000 zuwa naira 9,000, inda hakan ya sa mutane ba sa iya saye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan TsakiKiwoNomaSana"aTsada
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Su Ne Muradun Sinawa

Next Post

Nijeriya Ta Sake Zama Mamba A Hukumar Kula Da Harkokin Sufurin Jiragen Sama Ta Kasa Da Kasa 

Related

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kira Taron Manyan Kafafen Yada Labarai Kan Samar Da Wadataccen Abinci

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

7 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

1 week ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

1 week ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

1 week ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Next Post
Nijeriya Ta Sake Zama Mamba A Hukumar Kula Da Harkokin Sufurin Jiragen Sama Ta Kasa Da Kasa 

Nijeriya Ta Sake Zama Mamba A Hukumar Kula Da Harkokin Sufurin Jiragen Sama Ta Kasa Da Kasa 

LABARAI MASU NASABA

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir

May 18, 2025
Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

May 17, 2025
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

May 17, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 17, 2025
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

May 17, 2025
Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

May 17, 2025
Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

May 17, 2025
Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

May 17, 2025
Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

May 17, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.