• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Matakin Gina Titi Kilomita 108 Cikin Gaggawa

by Sulaiman and Leadership Hausa
11 months ago
in Labarai
0
Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Ɗauki Matakin Gina Titi Kilomita 108 Cikin Gaggawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya amince da aikin hanyar Magami zuwa Ɗansadau mai tsawon kilomita 108.

 

Gwamnan ya amince da aikin hanyar ne yayin da ya jagoranci taron Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara a ranar Litinin da ta gabata a gidan gwamnati da ke Gusau.

  • Kiran Tada Hankali A Zanga-zanga: Rundunar ‘Yansanda Ta Cafke Wani Dan TikTok A Filato
  • Kamfanin MTN Ya Rufe Ofishoshinsa A Fadin Nijeriya 

A cikin wata sanarwa da Mai Magana da Yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, an ɗauki aikin hanyar Magami zuwa Ɗansadau ne a matakin gaggawa domin magance matsalar tsaro da kuma bai wa al’ummar yankin fifiko don jin daɗin rayuwar su.

 

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Sanarwar ta ƙara da cewa, a tarona majalisar zaryarwar, an tattauna muhimman batutuwa da suka haɗa da yadda ake gudanar da kasafin kuɗi.

 

“Gwamna Dauda Lawal ne ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar Zamfara, wanda ya gudana jiya.

 

“A taron, gwamnan ya amince da sake gina hanyar Magami zuwa Ɗansadau.

 

“Aikin titin mai tsawon kilomita 108, kamar yadda aka bayyana a cikin kasafin kuɗin shekarar 2024, ma’aikatar ayyuka da samar da ababen more rayuwa ta samu amincewar gwamnan na fara aikin, tare da bin tsarin da ya dace na bayar da kwangila, da ba da izini da kuma takardar shaidar aiki ba tare da wata matsala ba daga Hukumar Sayen Kayayyakin Gwamnatin (BPP).

 

“Gwamnan ya amince da bayar da kwangilar ga kamfanin ‘Dantata and Sawoe Construction Co. Ltd’, a matsayin kwangilar da za a yi ta cikin watanni 18 a kan kuɗi Naira 81,189,223,505.73.”

 

Manyan abubuwan da aikin ya ƙunsa sun haɗa da; tsaftace dukkan wuraren da aikin zai shafa, cire kayan da ba su dace ba da maye gurbinsu, tare da ingantattun kayan da aka yarda da su, da samar da magudanan ruwa ingantattu, da sanya gadoji a wuraren da suka dace.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Me Ya Kawo Matasa Zuwa Yankin Xizang Na Kasar Sin?

Next Post

Me Ya Sa Sin Da Italiya Suke Dora Muhimmanci Kan “Ruhin Hanyar Siliki”?

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

4 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

12 hours ago
Next Post
Me Ya Sa Sin Da Italiya Suke Dora Muhimmanci Kan “Ruhin Hanyar Siliki”?

Me Ya Sa Sin Da Italiya Suke Dora Muhimmanci Kan “Ruhin Hanyar Siliki”?

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.