• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsaro Wani Hakki Ne Na Dan Adam

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tsaro Wani Hakki Ne Na Dan Adam
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Abokaina barka da karamar Sallah! Na ga wasu hotunan bukukuwan murnar Sallah da wasu abokai suka yi tare da iyalansu, ta shafukan sada zumunta. Na ji dadin yadda suke biki cikin wani yanayi na murna da kwanciyar hankali. Saboda kun san ba a ko ina ake iya yin haka ba.

Yanzu haka a kasar Sudan da ba ta da nisa da kasar Najeriya, ana ci gaba da fama da dauki ba dadi. Kana a Mali da Burkina Faso, su ma sun samu abkuwar hare-hare a kwanakin nan. Ko a wasu yankunan kasar Najeriya ma, hare-haren ’yan fashi da masu neman satar mutane na ci gaba da ci wa jama’a tuwo a kwarya.

  • Xi Jinping Ya Mikawa Dandalin Bayanai Na MDD Karo Na 4 Wasikar Taya Murna

Kowa ya sani, tsaro wani hakki ne na dan Adam, kuma tushen ci gaban al’umma. Saboda idan babu tsaro, ba za a iya rayuwa ba, balle ma a samu ci gaban sauran harkoki.
A wasu wurare, yanayi na tashin hankali ya kori masu neman zuba jari, abin da ya sa ake fuskantar rashin damar raya masana’antu, da karancin guraben aikin yi da za a iya samar wa matasa.

Daga baya, matasan da ba su da aikin yi su kan fara kokarin neman duk wata hanyar samun kudi, har ma wasunsu suka fara karya doka, lamarin da ke kara lalata yanayin tsaron da ake ciki. Ta wannan hanya, wadannan wurare sun tsunduma cikin da’irar faduwa, inda yanayi na yamutsi da talauci ke kara tsananta.

Yayin da a wasu wurare, mabambantan kasashe, da rukunoni ke gwabza fada a tsakaninsu, saboda kowanensu na neman tabbatar da tsaron kai. Sai dai fadan da suke yi ya sa tsaro ya zama wani abu mai nisa, wanda kusan ba za a iya tabawa ba.
Ta la’akari da wannan yanayin da ake ciki ne, ya sa kasar Sin gabatar da shawarar tabbatar da tsaron duniya, a shekara daya da ta gabata.

Labarai Masu Nasaba

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Babban makasudin shawarar shi ne, a yi kokarin samar da wani yanayi na tsaro na bai daya. Wato don tabbatar da tsaro a duniyarmu, ana bukatar samun tattaunawa, da hadin gwiwa tsakanin kasashe daban daban.

Dole ne a tabbatar da tsaron kowa, ta yadda tsaron zai iya dorewa. Saboda haka, ya kamata, mabambantan kasashe su kara kokarin musayar ra’ayi da hadin kai, da nacewa ga adalci, da bin ka’idojin kasa da kasa, da neman daidaita rikici kafin ya yi tsamari, ta yadda za a iya tabbatar da tsaron daukacin bil Adama cikin hadin gwiwa.

A nata bangare, kasar Sin ta ba da wannan shawara ta tabbatar da tsaro a duniya, ita ma ta aikata hakan kamar yadda ta fada. Cikin shekarar da ta wuce, mun gane ma idanunmu yadda kasashen Saudiya, da Iran, suka kawo karshen sa-in-sa a tsakaninsu, da farfado da huldar diplomasiyya, bisa sulhun da kasar Sin ta yi, da yadda kasar Sin ta yi kokarin neman sanya kura ta lafa a kasar Ukraine, tare da gabatar da wata muhimmiyar takardar bayani, wadda a cewar Stephane Dujarric, kakakin babban magatakardan MDD, wata muhimmiyar gudunmowa ce ga yunkuruin daidaita rikicin.

Ban da haka kuma, cikin wani dogon lokacin da ya gabata, kasar Sin ta yi kokarin hadin gwiwa da kasashen Afirka, da kasashe masu tasowa na sauran sassan duniya, a bangaren aikin tsaro da ba na gargajiya ba, wanda ya hada da yaki da ta’addanci, da samar da isashen abinci, da aikin jinya, da dai sauransu.

Inda kasar Sin ta tura sojojinta fiye da dubu 50 don halartar aikin wanzar da zaman lafiya da MDD take gudanarwa, da taimakawa kasashen Afirka horar da kwararru masu fasahohin aikin gona, da noman sabbin nau’ikan amfanin gona masu inganci, da samar da alluran rigakafin cutar COVID-19 fiye da biliyan 2.2 ga kasashe da kungiyoyi fiye da 120, da tura dimbin tawagogin likitoci zuwa kasashe daban daban, inda suka samar da hidimar jinya ga mutane kimanin miliyan 290.

Sai dai mun san ba za a iya tabbatar da tsaron duniya ta karfin wata kasa kadai ba. Aikin na bukatar hadin gwiwar kasashe daban daban. A nan, mun gamu da katari, ganin yadda mutanen duniya ke ci gaba da daukaka zaman lafiya da bunkasuwar tattalin arziki, a wannan zamanin da muke ciki.

Yanzu haka, wasu kasashe da kungiyoyi fiye da 80 sun yaba da kasar Sin, da nuna mata goyon baya, kan shawarar da ta gabatar ta tabbatar da tsaro a duniya.

Hakan ya nuna cewa, kasashe daban daban sun fara cimma ra’ayi daya, wato manufar yin babakere a duniya, da ta sa hannu cikin harkokin gida na sauran kasashe, da yin takara cikin wani mummunan yanayi, da ra’ayi na son kai, kawai suna lahanta tsaro na kowa. Yayin da ra’ayin kasar Sin na tabbatar da tsaro na bai daya, ya zama wata manufa ta girmama mutunci na kowace kasa, da hakki na tushe na daidaikun mutane. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tanzaniya Ta Yi Maraba Da Zuwan Tawagogin Yawon Shakatawa Na Sin

Next Post

Sin Ta Kaddamar Da Ranar Samaniya Ta Hanyar Baje Hotunan Duniyar Mars

Related

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

1 hour ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

20 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

21 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

22 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

23 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

1 day ago
Next Post
Sin Ta Kaddamar Da Ranar Samaniya Ta Hanyar Baje Hotunan Duniyar Mars

Sin Ta Kaddamar Da Ranar Samaniya Ta Hanyar Baje Hotunan Duniyar Mars

LABARAI MASU NASABA

Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

Yadda YaÆ™in Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin ArziÆ™in Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

June 29, 2025
Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 YaÆ™i Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin ArziÆ™in Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.