• English
  • Business News
Monday, November 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Dan Wasan Kwallon Kafa Na Kano Pillars, Kofarmata, Ya Rasu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kofarmata

Allah ya yi rasuwa wa tsohon dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars, Bello Musa Kofarmata.

Ya rasu ne a daren ranar Talata yana da shekara 34 a duniya bayan wata yar gajeruwar rashin lafiya da ta sameshi a gidansa da ke unguwar Kofarmata a jihar Kano.

  • An Mayar Da Tubabbun Mayakan Boko Haram 3,500 Unguwanninsu A Jihar Borno

Tsohon mataimakin shugaban kungiyar marubuta labarin wasanni na shiyyar Arewa Maso Yamma, Ado Salifu shi ne ya tabbatar wa LEADERSHIP rasuwar, ya ce, tunin aka yi jana’izar mamacin da safiyar ranar Laraba kamar yadda addinin musulunci ya tanadar a Kofarmata da ke Kano.

Kofarmata
Marigayi, Bello Musa Kofarmata

Kofarmata dai ya shiga kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ce a shekarar 2007 ya kuma taimaka wa kungiyar wajen samun nasara a yayin gasar Premier league ta Nijeriya da aka gudanar 2007/2008 da kwallaye 11. Kuma shi ne wanda ya fi zura kwallaye da suka kai su ga nasara.

Ya bar kungiyar Kano Pillars a shekarar 2010 inda ya shiga kungiyar kwallon kafa ta Heartland FC da ke Owerri daga baya ya sake barinta a shekarar 2012 kuma ya shiga kungiyar Elkanemi Warriors da ke Maiduguri.

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Ya sake komawa tsohowar kungiyarsa kafin daga bisani ya fita daga kasar Nijeriya tare da sanya hannun kwantiragi da kungiyar IK Start of Norway.

Marigayi Kofarmata ya kasance cikin ‘yan wasannin Nijeriya (Maza) ‘U20’ da suka taka leda, Flying Eagles squad zuwa Canada 2007 FIFA U20 World Cup.

Ya buga wa manyan ‘yan wasan Nijeriya Super Eagles wasa guda daya, a wasan sada zumunci da suka yi da Jamhuriyar demokraxiyya Congo da suka samu ci 5-2 a Abuja a watan Maris na 2010 da sauran wasanni da dama da ya nuna bajintarsa a ciki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya
Manyan Labarai

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
Manyan Labarai

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
Manyan Labarai

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Next Post
EFCC Na Binciken Ba’asin Aikin Tashar Wutar Lantarki Ta Mambila – Minista

EFCC Na Binciken Ba'asin Aikin Tashar Wutar Lantarki Ta Mambila - Minista

LABARAI MASU NASABA

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya

November 2, 2025
Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

November 2, 2025
Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar

November 2, 2025
Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

November 2, 2025
Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

November 2, 2025
Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

Yadda Za Ku Hada Fab Biskit

November 2, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su

November 2, 2025
Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Gidauniyar IRM Da KADCHMA Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

November 2, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.