• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Daraktan Yakin Neman Zaben Tsohon Gwamnan Bauchi Ya Koma Labour Party

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Bauchi

Tsohon daraktan yakin zaben tsohon gwamnan jihar Bauchi, Muhammadu Abdullahi Abubakar, wato Alhaji Garba Sarki Akuyam, ya shelanta ficewa daga jam’iyyar APC tare komawa cikin jam’iyyar Labour Pary (LP) tare da daruruwan magoya bayansa.

Akuyam wanda tsohon kwamishinan kudi da ci gaban tatttalin arziki na jihar Bauchi ne, ya shelanta komawa LP ne a ziyarar da ya kai wa shugaban jam’iyyar a jihar Bauchi, Barista Hussaini Saraki a ofishin jam’iyyar jiya, yana mai cewa, ya tuntubi masu ruwa da tsaki da magoya bayansa kafin daukan wannan matakin.

  • ‘Yan Jihar Bauchi Sun Yabawa Buhari Kan Amincewa Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsohuwar 200
  • Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Akuyam ya bayyana cewar dalilansa na ficewa daga cikin APC sun hada har da rashin gamsuwarsa da yadda ake gudanar da lamura a cikin jam’iyyar a matakin jiha da ma kasa, kana ya bibiyi tarihin Peter Obi da irin nasarorin da ya cimma a rayuwarsa, don haka yana da kwarin guiwar Peter zai iya shawo kan matsalolin da suke addabar kasar nan.

Ya kara da cewa a matsayinsa na wanda ya ke da gogewa a bangaren siyasa da jagoranci a jam’iyyar APC har ta kai ga samun nasara a zaben 2015 da ya gudana a jihar Bauchi, bai gamsu da yadda ake tafiyar da lamura a cikin jam’iyyar ba a halin yanzu, don haka shi da daruruwan magoya bayansa suka fice daga cikin jam’iyyar.

Ya kuma kara da cewa, abokin takarar Peter, Yusuf Datti Baba Ahmed, ya fito daga fitacciyar zuri’a a arewa kuma yana da kyakkyawar alaka da su, don haka ya ga dacewar ya koma cikin jam’iyyar LP domin bada tashi gudunmawar wajen ganin sun samu nasarar lashe zabukan da ke tafe.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Garba Sarki Akuyam tsohon kwamishinan bunkasa yankunan karkara na jihar Bauchi ne, ya bada tabbacin cewa zai yi dukkanin mai yiyuwa domin ganin nasarar jam’iyyar a dukkanin matakai, ya kuma nemi alfarmar jagororin jam’iyyar da su amince da shi hannu biyu-biyu.

A jawabinsa na maraba, shugaban jam’iyyar Labour Party a jihar Bauchi, Barista Hussaini Saraki, ya shaida cewar wannan babban nasara ce a garesu kuma yana mai bai wa Akuyam da sauran magoya bayansa tabbacin samun adalci a jam’iyyar.

“Tabbas samun kwararren masanin siyasa kuma masanin tattalin arziki a cikin jam’iyyarmu babban nasara ce a garemu. Sannan, yadda jama’a suke tururuwar shigowa cikin LP a jihar Bauchi na nuna mana irin gagarumar nasarar da za mu iya samu a zaben da ke tafe.”

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na samun nasarar jam’iyyar a dukkanin matakai, yana mai kira ga sauran jama’a da su shigo a dama da su domin ceto kasar nan daga halin da take ciki.

Saraki daga bisani ya jinjina wa Sarkin Akuyam bisa daukar wannan matakin fi dacewa domin hada karfi da karfe wajen ceto Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP
Siyasa

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan
Manyan Labarai

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
Siyasa

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

October 11, 2025
Next Post
An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

Kowacce Mace Tauraruwa Ce A Kasar Sin

October 14, 2025
Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya

October 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Benin A Uyo

October 14, 2025
Asuu

An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 

October 14, 2025
Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata

October 14, 2025
Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

Majalisar Wakilai Ta Buƙaci Hukumomin Tsaro Su Kai Agajin Gaggawa A Sakkwato

October 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Ghana Da Firaministar Mozambique

October 14, 2025
‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

October 14, 2025
An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.