• English
  • Business News
Thursday, May 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Daraktan Yakin Neman Zaben Tsohon Gwamnan Bauchi Ya Koma Labour Party

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Siyasa
0
Tsohon Daraktan Yakin Neman Zaben Tsohon Gwamnan Bauchi Ya Koma Labour Party
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon daraktan yakin zaben tsohon gwamnan jihar Bauchi, Muhammadu Abdullahi Abubakar, wato Alhaji Garba Sarki Akuyam, ya shelanta ficewa daga jam’iyyar APC tare komawa cikin jam’iyyar Labour Pary (LP) tare da daruruwan magoya bayansa.

Akuyam wanda tsohon kwamishinan kudi da ci gaban tatttalin arziki na jihar Bauchi ne, ya shelanta komawa LP ne a ziyarar da ya kai wa shugaban jam’iyyar a jihar Bauchi, Barista Hussaini Saraki a ofishin jam’iyyar jiya, yana mai cewa, ya tuntubi masu ruwa da tsaki da magoya bayansa kafin daukan wannan matakin.

  • ‘Yan Jihar Bauchi Sun Yabawa Buhari Kan Amincewa Da Ci Gaba Da Amfani Da Tsohuwar 200
  • Dan Takarar Gwamnan ZLP A Bauchi Ya Musanta Janye Takararsa

Akuyam ya bayyana cewar dalilansa na ficewa daga cikin APC sun hada har da rashin gamsuwarsa da yadda ake gudanar da lamura a cikin jam’iyyar a matakin jiha da ma kasa, kana ya bibiyi tarihin Peter Obi da irin nasarorin da ya cimma a rayuwarsa, don haka yana da kwarin guiwar Peter zai iya shawo kan matsalolin da suke addabar kasar nan.

Ya kara da cewa a matsayinsa na wanda ya ke da gogewa a bangaren siyasa da jagoranci a jam’iyyar APC har ta kai ga samun nasara a zaben 2015 da ya gudana a jihar Bauchi, bai gamsu da yadda ake tafiyar da lamura a cikin jam’iyyar ba a halin yanzu, don haka shi da daruruwan magoya bayansa suka fice daga cikin jam’iyyar.

Ya kuma kara da cewa, abokin takarar Peter, Yusuf Datti Baba Ahmed, ya fito daga fitacciyar zuri’a a arewa kuma yana da kyakkyawar alaka da su, don haka ya ga dacewar ya koma cikin jam’iyyar LP domin bada tashi gudunmawar wajen ganin sun samu nasarar lashe zabukan da ke tafe.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

Garba Sarki Akuyam tsohon kwamishinan bunkasa yankunan karkara na jihar Bauchi ne, ya bada tabbacin cewa zai yi dukkanin mai yiyuwa domin ganin nasarar jam’iyyar a dukkanin matakai, ya kuma nemi alfarmar jagororin jam’iyyar da su amince da shi hannu biyu-biyu.

A jawabinsa na maraba, shugaban jam’iyyar Labour Party a jihar Bauchi, Barista Hussaini Saraki, ya shaida cewar wannan babban nasara ce a garesu kuma yana mai bai wa Akuyam da sauran magoya bayansa tabbacin samun adalci a jam’iyyar.

“Tabbas samun kwararren masanin siyasa kuma masanin tattalin arziki a cikin jam’iyyarmu babban nasara ce a garemu. Sannan, yadda jama’a suke tururuwar shigowa cikin LP a jihar Bauchi na nuna mana irin gagarumar nasarar da za mu iya samu a zaben da ke tafe.”

Ya kuma nuna kwarin guiwarsa na samun nasarar jam’iyyar a dukkanin matakai, yana mai kira ga sauran jama’a da su shigo a dama da su domin ceto kasar nan daga halin da take ciki.

Saraki daga bisani ya jinjina wa Sarkin Akuyam bisa daukar wannan matakin fi dacewa domin hada karfi da karfe wajen ceto Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’in MDD: Fasahohin Sin Za Su Taimaka Wa Afirka Tinkarar Matsalar Sauyin Yanayi

Next Post

An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

Related

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye
Siyasa

Dalilin Gwamnatin Kano Na Haramta Shirye-shiryen Siyasa Kai Tsaye

11 hours ago
Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi
Siyasa

Gwamna Fintiri Ba Zai Bar PDP Ba – Humwashi

4 days ago
Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani
Siyasa

Gwamna Abba Kabir Ya Mayar Wa Da Bappa Bichi Martani

4 days ago
Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba
Labarai

Atiku Ne Rikitacce Ba Tinubu Ba

6 days ago
Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka
Siyasa

Mataimakin Gwamnan Neja Ya Ki Halartar Bikin Ranar Ma’aikata, Ana Zargin Akwai Takun Saka

1 week ago
‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung
Siyasa

‘Yan Siyasa Na Komawa APC Don Buƙatar Kansu, Ba Don Jama’a Ba – Dalung

1 week ago
Next Post
An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

An Bude Baje Kolin Fina-finai Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya”

LABARAI MASU NASABA

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

Zamalek Ta Sallami Tsohon Kocin Super Eagles, Peseiro

May 8, 2025
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

May 8, 2025
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

May 8, 2025
Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.