• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Kwamishinan Tambuwal Ya Musanta Zargin Hannun Jarin Biliyan 16

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto and Sulaiman
1 year ago
Tambuwal

Tsohon Kwamishinan Kudi na jihar Sakkwato, Hon. Abdussamad Dasuki ya bayyana cewar, babu kamshin gaskiya ko kadan kan ikirarin sayar da hannun jarin naira biliyan 16 a lokacin gwamnatin Tambuwal kamar yadda ya bayyana a yayin bayar da shaida a gaban hukumar binciken ayyukan tsohuwar gwamnatin jihar daga 2015- 2023. 

 

Dasuki, wanda a yanzu ke wakiltar Kebbe/Tambuwal a majalisar wakilai ta tarayya, ya bayyana cewar ba ya da masaniyar hannun jarin naira biliyan 16, abin da ya sani hannun jarin naira biliyan uku ne da doriya. Ya ce kamfanin saka jari na jiha kai tsaye yana bayar da bayani ne a fadar gwamnati ba a karkashin ma’aikatar kudi ba wadda ya yi wa Kwamishina daga Yuni 2019 zuwa Maris 2022.

  • Manufar “Sabon Karfin Samar Da Hajoji Da Hidimomi Masu Karko” Za Ta Samar Da Ci Gaban Da Duniya Ke Muradi
  • Ambaliya: Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Ta Bai Wa Maiduguri Tallafin Miliyan 20

Ya ce shugaban kamfanin saka jari ya fada masa cewar, baki daya hannun jarin na naira biliyan uku ne da doriya wadanda aka hade su a waje daya a 2017 aka kuma dauke su daga ma’aikatar kudi aka mayar da su a karkashin kamfanin saka jari, ya kuma ce ba ya da masaniyar ko an sayar da hannun jarin.

 

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Ya ce “A lokacin cutar korona a 2020 wadda tattalin arzikin Nijeriya da duniya baki daya ya tabarbare, an samu karancin kudaden kason wata- wata daga gwamnatin Tarayya da karancin haraji, kuma an ba mu umurnin fara biyan mafi karancin albashi na naira dubu 30.”

 

Dasuki ya bayyana cewar, a bisa wannan dalilin ne Tambuwal ya bai wa kamfanin saka jari umurnin ba su naira biliyan biyu wadanda da farko aka ba su naira biliyan 1, daga baya aka ba su naira miliyan 500 wadanda aka saka a asusun babban akawun gwamnati domin gudanar da muhimman ayyukan raya jiha, biyan albashi da sauransu.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Jami’an ‘Yansanda 5 Sun Mutu, 11 Sun Jikkata Sakamakon Hatsarin Mota A Kano

Jami’an ‘Yansanda 5 Sun Mutu, 11 Sun Jikkata Sakamakon Hatsarin Mota A Kano

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.