• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsokaci Kan Tasirin Noman Kabeji A Nijeriya

by Abubakar Abba
11 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsokaci Kan Tasirin Noman Kabeji A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fannin noman Kabeji, abu ne sananne a dukkanin fadin wannan kasa da muke ciki, musamman sakamakon yakinin da wasu ke da shi na cewa; ya fi yin kyau idan aka shuka shi a Jihar Filato, amma a hankali sauran wasu manoma a nan Nijeriya; su ma suka rungumi nomansa.

Har ila yau, akwai wasu daidaikun mutane da ke noman sa a Kudu Maso Yammacin wannan kasa, haka zalika za a iya noman sa a kowane yanki da muke da a fadin wannan kasa.

  • Sin Ba Za Ta Canza Matsayarta Game Da Mayar Da Hankali Kan Kasashe Masu Tasowa Ba
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Kabeji ya fi saurin girma a ma’aunin yanayin da ya kai daga 55 zuwa 60, inda kuma akwai nau’ikansa da ke saurin girma a ma’aunin yanayin da ya kai daga 20 zuwa 25.

Har wa yau, nomansa ya samo asali ne daga farkon kafuwar Kasar Girka da kuma Kasar Romaniya, inda nomansa ya ci gaba da yaduwa zuwa kasar Birtaniya, ya kuma ci gaba da yaduwa zuwa sauran wasu kasashe.

Akasari a Nahiyar Afirka, musaman a Nijeria; ana yawan yin amfani da shi a lokutan bukukuwan Sallah ko na Kiristimeti da sauransu, ya kuma kasance yana dauke da sinadarin ‘calcium da ke inganta lafiyar jikin Dan’adam.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Bugu da kari, nomansa ba shi da wata wahala; sannan kuma akwai sauki wajen kula da shi bayan an shuka shi. Haka nan kuma, ba sai kana da kudi mai yawa za ka iya fara yin nomansa ba, ko a bayan dakinka za ka iya noma shi.

Gyaran Gona:

Ana iya shuka shi a kan kowace irin kasar noma, kadai abin da ake bukata shi ne; bayan manomi ya gyara gona, sai ya shuka Irin da yake da shi. Haka nan, manomi zai iya amfani da motar Tarakta; don yin gyran gonarsa, musaman idan kasar noman na da tsauri sai ya yi mata haro; ya shuka Irinsa.

Shuka Shi:

Ramin da za ka shuka Irin nasa, ana so ya kai zurfin kimanin daga kafa biyu zuwa uku, idan kuma za ka yi renon Irin ne; ana so ka saka shi a cikin buhu ko kuma cikin ledar da ake yin renon Irin, daga nan bayan sati uku zuwa hudu sai ka canza masa wani gurin daban; bayan ya kai tsawon santi mita 14 zuwa 16.

Yi Masa Ban Ruwa:

Ana so a rika yi masa ban ruwa a kai a kai duk bayan sati guda, ganin cewa Kabeji na bukatar ruwan da ya kai santi mita 3.8, musamman ganin cewa; Kabeji ba ya son yanayi na fari.

Zuba Masa Taki:

Ana so tun farkon lokacin da aka shuka Irinsa, a zuba masa takin zamani, musamman don ya yi saurin girma; inda kuma bayan sati uku da canza masa wani gurin, ana so a kara zuba masa wani takin.

Kare Shi Daga Kamuwa Da Cututtuka:

Kamar sauran amfanin gona, shi ma Kabeji akwai cututtukan da ke yi masa illa; kamar irin wadanda ake kira a turance ‘flea beetles’, da sauran makamantansu.

Lokacin Girbe Shi:

Ana yi masa girbi bayan ya gama girma baki-daya, sai dai ya danganta da nau’in Irin da aka yi amfani da shi, haka nan bayan girbe shi, ana iya samun daga tan 70 zuwa 80.

Sayar Da Shi:

Manomin da ya noma shi, zai iya sayar da shi ga ‘yan kasuwar da ke yin sana’arsa ko a manyan shaguna da gidajen sayar da abinci ko a Otel ko kuma ya yi tallansa a kafar yanar Gizo.

Adana Shi:

Bayan an gibe shi, ana kuma bukatar a adana shi a wurin da yake da sanyi, za kuma a iya adana shi har zuwa wata uku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KabejiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Isra’ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

Next Post

Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Related

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

2 days ago
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

2 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

1 week ago
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

1 week ago
Gwamnatin Kogi Ta Yi HaÉ—in Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Kogi Ta Yi HaÉ—in Gwuiwa Don Fara Fitar Da Amfanin Gona

1 week ago
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi
Noma Da Kiwo

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

2 weeks ago
Next Post
Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

October 5, 2025
Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

Ko Kin San… Amfanin Sabaya Ga Mace?

October 5, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.