• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsokaci Kan Tasirin Noman Kabeji A Nijeriya

by Abubakar Abba
11 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsokaci Kan Tasirin Noman Kabeji A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fannin noman Kabeji, abu ne sananne a dukkanin fadin wannan kasa da muke ciki, musamman sakamakon yakinin da wasu ke da shi na cewa; ya fi yin kyau idan aka shuka shi a Jihar Filato, amma a hankali sauran wasu manoma a nan Nijeriya; su ma suka rungumi nomansa.

Har ila yau, akwai wasu daidaikun mutane da ke noman sa a Kudu Maso Yammacin wannan kasa, haka zalika za a iya noman sa a kowane yanki da muke da a fadin wannan kasa.

  • Sin Ba Za Ta Canza Matsayarta Game Da Mayar Da Hankali Kan Kasashe Masu Tasowa Ba
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Kabeji ya fi saurin girma a ma’aunin yanayin da ya kai daga 55 zuwa 60, inda kuma akwai nau’ikansa da ke saurin girma a ma’aunin yanayin da ya kai daga 20 zuwa 25.

Har wa yau, nomansa ya samo asali ne daga farkon kafuwar Kasar Girka da kuma Kasar Romaniya, inda nomansa ya ci gaba da yaduwa zuwa kasar Birtaniya, ya kuma ci gaba da yaduwa zuwa sauran wasu kasashe.

Akasari a Nahiyar Afirka, musaman a Nijeria; ana yawan yin amfani da shi a lokutan bukukuwan Sallah ko na Kiristimeti da sauransu, ya kuma kasance yana dauke da sinadarin ‘calcium da ke inganta lafiyar jikin Dan’adam.

Labarai Masu Nasaba

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

Bugu da kari, nomansa ba shi da wata wahala; sannan kuma akwai sauki wajen kula da shi bayan an shuka shi. Haka nan kuma, ba sai kana da kudi mai yawa za ka iya fara yin nomansa ba, ko a bayan dakinka za ka iya noma shi.

Gyaran Gona:

Ana iya shuka shi a kan kowace irin kasar noma, kadai abin da ake bukata shi ne; bayan manomi ya gyara gona, sai ya shuka Irin da yake da shi. Haka nan, manomi zai iya amfani da motar Tarakta; don yin gyran gonarsa, musaman idan kasar noman na da tsauri sai ya yi mata haro; ya shuka Irinsa.

Shuka Shi:

Ramin da za ka shuka Irin nasa, ana so ya kai zurfin kimanin daga kafa biyu zuwa uku, idan kuma za ka yi renon Irin ne; ana so ka saka shi a cikin buhu ko kuma cikin ledar da ake yin renon Irin, daga nan bayan sati uku zuwa hudu sai ka canza masa wani gurin daban; bayan ya kai tsawon santi mita 14 zuwa 16.

Yi Masa Ban Ruwa:

Ana so a rika yi masa ban ruwa a kai a kai duk bayan sati guda, ganin cewa Kabeji na bukatar ruwan da ya kai santi mita 3.8, musamman ganin cewa; Kabeji ba ya son yanayi na fari.

Zuba Masa Taki:

Ana so tun farkon lokacin da aka shuka Irinsa, a zuba masa takin zamani, musamman don ya yi saurin girma; inda kuma bayan sati uku da canza masa wani gurin, ana so a kara zuba masa wani takin.

Kare Shi Daga Kamuwa Da Cututtuka:

Kamar sauran amfanin gona, shi ma Kabeji akwai cututtukan da ke yi masa illa; kamar irin wadanda ake kira a turance ‘flea beetles’, da sauran makamantansu.

Lokacin Girbe Shi:

Ana yi masa girbi bayan ya gama girma baki-daya, sai dai ya danganta da nau’in Irin da aka yi amfani da shi, haka nan bayan girbe shi, ana iya samun daga tan 70 zuwa 80.

Sayar Da Shi:

Manomin da ya noma shi, zai iya sayar da shi ga ‘yan kasuwar da ke yin sana’arsa ko a manyan shaguna da gidajen sayar da abinci ko a Otel ko kuma ya yi tallansa a kafar yanar Gizo.

Adana Shi:

Bayan an gibe shi, ana kuma bukatar a adana shi a wurin da yake da sanyi, za kuma a iya adana shi har zuwa wata uku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KabejiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Isra’ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

Next Post

Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Related

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Bukatar Manoma Su Rika Yi Wa Mangwaro Ban-ruwa

1 week ago
Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON
Noma Da Kiwo

Muna Bukatar Karin Hekta 500,000 Domin Noman Kwakwar Manja – POFON

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

3 weeks ago
Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025
Noma Da Kiwo

Ya Zama Wajibi Nijeriya Ta Cimma Wa’adin Tura Cocoa Tarayyar Turai A Disambar 2025

3 weeks ago
Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba
Noma Da Kiwo

Kwararre Ya Ja Hankali Kan Sayar Da Takin Zamani Da Ba A Tantace Shi Ba

4 weeks ago
Manoman Doya 100 A Jihar Nasarawa Suka Amfana Da Horon Cibiyar NEPC
Noma Da Kiwo

Hukumar NABDA Ta Bukaci Musulmi Su Cire Fargabar Amfani Da Fasahar Alkinta Halittu

4 weeks ago
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Tinubu Ya Naɗa Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.