• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsokaci Kan Tasirin Noman Kabeji A Nijeriya

by Abubakar Abba
7 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Tsokaci Kan Tasirin Noman Kabeji A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fannin noman Kabeji, abu ne sananne a dukkanin fadin wannan kasa da muke ciki, musamman sakamakon yakinin da wasu ke da shi na cewa; ya fi yin kyau idan aka shuka shi a Jihar Filato, amma a hankali sauran wasu manoma a nan Nijeriya; su ma suka rungumi nomansa.

Har ila yau, akwai wasu daidaikun mutane da ke noman sa a Kudu Maso Yammacin wannan kasa, haka zalika za a iya noman sa a kowane yanki da muke da a fadin wannan kasa.

  • Sin Ba Za Ta Canza Matsayarta Game Da Mayar Da Hankali Kan Kasashe Masu Tasowa Ba
  • Gwamnatin Tarayya Da Google Sun Bullo Da Hanyar Samar Wa Da Matasa 2,500 Aikin Dogaro Da Kai

Kabeji ya fi saurin girma a ma’aunin yanayin da ya kai daga 55 zuwa 60, inda kuma akwai nau’ikansa da ke saurin girma a ma’aunin yanayin da ya kai daga 20 zuwa 25.

Har wa yau, nomansa ya samo asali ne daga farkon kafuwar Kasar Girka da kuma Kasar Romaniya, inda nomansa ya ci gaba da yaduwa zuwa kasar Birtaniya, ya kuma ci gaba da yaduwa zuwa sauran wasu kasashe.

Akasari a Nahiyar Afirka, musaman a Nijeria; ana yawan yin amfani da shi a lokutan bukukuwan Sallah ko na Kiristimeti da sauransu, ya kuma kasance yana dauke da sinadarin ‘calcium da ke inganta lafiyar jikin Dan’adam.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

Bugu da kari, nomansa ba shi da wata wahala; sannan kuma akwai sauki wajen kula da shi bayan an shuka shi. Haka nan kuma, ba sai kana da kudi mai yawa za ka iya fara yin nomansa ba, ko a bayan dakinka za ka iya noma shi.

Gyaran Gona:

Ana iya shuka shi a kan kowace irin kasar noma, kadai abin da ake bukata shi ne; bayan manomi ya gyara gona, sai ya shuka Irin da yake da shi. Haka nan, manomi zai iya amfani da motar Tarakta; don yin gyran gonarsa, musaman idan kasar noman na da tsauri sai ya yi mata haro; ya shuka Irinsa.

Shuka Shi:

Ramin da za ka shuka Irin nasa, ana so ya kai zurfin kimanin daga kafa biyu zuwa uku, idan kuma za ka yi renon Irin ne; ana so ka saka shi a cikin buhu ko kuma cikin ledar da ake yin renon Irin, daga nan bayan sati uku zuwa hudu sai ka canza masa wani gurin daban; bayan ya kai tsawon santi mita 14 zuwa 16.

Yi Masa Ban Ruwa:

Ana so a rika yi masa ban ruwa a kai a kai duk bayan sati guda, ganin cewa Kabeji na bukatar ruwan da ya kai santi mita 3.8, musamman ganin cewa; Kabeji ba ya son yanayi na fari.

Zuba Masa Taki:

Ana so tun farkon lokacin da aka shuka Irinsa, a zuba masa takin zamani, musamman don ya yi saurin girma; inda kuma bayan sati uku da canza masa wani gurin, ana so a kara zuba masa wani takin.

Kare Shi Daga Kamuwa Da Cututtuka:

Kamar sauran amfanin gona, shi ma Kabeji akwai cututtukan da ke yi masa illa; kamar irin wadanda ake kira a turance ‘flea beetles’, da sauran makamantansu.

Lokacin Girbe Shi:

Ana yi masa girbi bayan ya gama girma baki-daya, sai dai ya danganta da nau’in Irin da aka yi amfani da shi, haka nan bayan girbe shi, ana iya samun daga tan 70 zuwa 80.

Sayar Da Shi:

Manomin da ya noma shi, zai iya sayar da shi ga ‘yan kasuwar da ke yin sana’arsa ko a manyan shaguna da gidajen sayar da abinci ko a Otel ko kuma ya yi tallansa a kafar yanar Gizo.

Adana Shi:

Bayan an gibe shi, ana kuma bukatar a adana shi a wurin da yake da sanyi, za kuma a iya adana shi har zuwa wata uku.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KabejiNoma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Isra’ila Ta Kai Wa Iran; Saudiyya Ta Yi Jawabi

Next Post

Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Gabatar Da Wasu Shirye-shirye Na Bunƙasa Kiwon Shanu

4 days ago
Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Taimaka Wa Masu Kiwon Kifi Domin Jurewa Sauyin Yanayi

5 days ago
Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
Noma Da Kiwo

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

5 days ago
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Noma Da Kiwo

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

6 days ago
Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Dabarun Gargajiya Domin Jawo Hankalin Zuma

2 weeks ago
Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja
Noma Da Kiwo

Ambaliya: Yankunan Da Ba Za Su Yi Noma A Kakar Bana Ba A Jihar Neja

2 weeks ago
Next Post
Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

Tinubu Ya NaÉ—a Sunday Dare a Matsayin Mai Magana Da Yawunsa

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don YaÆ™ar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.