• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tubabben Kwamandan Boko Haram Ya Bayyana Ta’asar Da Suka Tafka A Sambisa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Tubabben Kwamandan Boko Haram Ya Bayyana Ta’asar Da Suka Tafka A Sambisa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

Wasu daga cikin tsofaffin kwamandojin kungiyar Jama’atu Ahlussunnah lil’da’wati wal jihad da aka fi sani da Boko Haram sun bayyana nadamar irin ta’addancin da suka tafka a matsayinsu na mayakan kungiyar a baya.

Da suke tattaunawa da sashen Hausa na Muryar Amurka, daya daga cikin hadiman dake zama daya daga cikin hadiman tsohon shugaban kungiyar Abubakar Shekau, kuma daya daga cikin wadanda suka sace daliban Chibok, ya ce abin da suka yi a baya hakika bai dace ba, kuma babban abin takaici ne.

  • Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba
  • Cinikayyar Waje Ta Sin Ta Karu Da Kaso 5.7 A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Ya ce ya san Abubakar Shekau shekaru da dama kafin ma a fara rikicin na Arewa  maso Gabas, ko da aka ji wa shekau din rauni, an kawo shi Damaturu, inda yake jinya kuma a lokacin shike yi masa ‘yan aikace-aikace da wanki da da sauransu.

Bayan da kuma Shekau ya koma daji su kan aika masa da kudi don biyan bukatun yau da kullum kafin daga bisani shima ya bisu dajin, inda bayan samun horo, shima ya zama cikakken kwamandan dake jagorantar kai hare- hare.

Wannan tsohon kwamandan da ya ce ya jagoranci kai hare-hare a sassan Arewa maso Gabas da dama, ya yi ikirarin kashe fararen hula da sojojin da bai san adadinsu ba, al’amarin kuma da ya ce yana matukar bakin cikin hakan.

Bugu da kari, ya kuma yi bayanin yadda ya taka rawa yayin sace daliban Chibok inda suka kai su dajin Sambisa, koda yake ya ce shi bai auri ko daya ba, amma abokansa da dama sun aure su.

Ya ce babban abin da ya sa ya fice daga kungiyar ta’addancin shi ne yadda ake sa su karkashe mutane wasu ma ta hanyar yankan rago ba gaira ba dalili.

Da kuma yake amsa tambayar ko ina Leah Sheribu take? daliba zaya tilo daga cikin daliban Dapchi da ta rage a hanun yan ta’addan, wannan tubabben kwamandan na Boko Haram ya ce LEAH tana hanun mayakan Boko Haram tsagin ISWAP a yankin tafkin Tchadi.

Ya ce abokansu ne ke rike da ita, kuma sun mata aure har ta haifi yara biyu, namiji da mace, koda yake mijinta na farko ya rasu, amma wani dan ta’addan ya sake aure ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramKwamandaSambisaTa'asa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Kamata Manchester United Ta Kori Erik ten Hag?

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Biya Wa Ɗalibai 1,740 Kuɗin Makaranta A Jami’ar Ilimi Ta Sa’adatu Rimi

Related

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

2 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

2 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

3 weeks ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 months ago
Next Post
Kotu Ta Aike Da Ramlat Princess Zuwa Gidan Gyaran Hali Na Kano Tsawon Watanni Bakwai

Gwamnatin Kano Ta Biya Wa Ɗalibai 1,740 Kuɗin Makaranta A Jami'ar Ilimi Ta Sa'adatu Rimi

LABARAI MASU NASABA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

July 25, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Dangote Ya Ajiye Muƙamin Shugabancin Kamfaninsa Na Siminti

July 25, 2025
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

July 25, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

July 25, 2025
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

July 25, 2025
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.