• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turmutsutsin Rabon Kayan Tallafi: Alama Ce Na Yadda Gwamnatin APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci – PRP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PRP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PRP ta jajantawa iyalan ‘yan Nijeriya da suka mutu a turmutsitsin da ya faru a Ibadan, Abuja, da kuma Jihar Anambra, inda ta ce wannan mummunan lamari ya nuna irin talaucin da jam’iyyar APC mai mulki a karkashin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ‘yan Nijeriya a ciki bayan cire tallafin man fetur da kuma aiwatar da wasu manufofin da ba su dace ba wadanda suka yi illa ga ‘yan kasa.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Kwamared Muhammed Ishak, ya fitar wanda aka raba wa ‘yan jarida a Abuja, yayin da ta dora wa gwamnatin tarayya alhakkin wannan lamarin, ta ce ya kamata shugabanni a matakai daban-daban na gwamnati su farka daga dogon barci da suke ciki tare da dauki matakai na gaggawa don magance tushen ire-iren wadannan al’amuran da suke faruwa a kasar nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Shinkafar Kirsimeti A Kaduna
  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti

“Jam’iyyar PRP tana mika jajenta ga iyalai da al’ummomin da suka mutu a wani mummunan turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafi a Ibadan ta Jihar Oyo, da Abuja da kuma Anambra. Wadannan munanan abubuwan da suka faru, musamman a Abuja da Anambra, na nuna matukar damuwa da yanayin da ‘yan Nijeriya da suka tsinci kawunansu a cikin a gwamnatin APC.

“Lamarin ya nuna yadda tsananin talauci da fatara da ke wanzuwa a cikin al’ummarmu, al’amuran da ya ta’azzara saboda rashin shugabanci na tsawon shekaru a kasar nan.

“Yayin da muke alhinin rayukan da aka rasa kan wannan lamari, dole ne mu kuma gane cewa wadannan bala’o’i na nuni ne da irin rikicin da al’umma suka tsinci kansu a ciki. Irin wannan lamari yana bukatar daukar matakin gaggawa daga wurin gwamnati a matakai daban-dabn da na al’umma gaba daya. Abubuwan da ke faruwa suna fallasa gazawar ba da fifiko ga walwala da amincin ‘yan kasa a cikin matsanancin yanayin zamantakewa da tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

“Jam’iyyar PRP ta dora wa gwamnatin tarayya da shugabancinta laifi, musamman Shugaban kasa Bola Ahmed Bola, wanda ya ingiza miliyoyin ‘yan Nijeriya ciki bakin talauci, biyo bayan cire tallafin man fetur da aiwatar da wasu manufofin da suka yi tasiri ga marasa karfi a cikinmu. Irin wadannan manufofin sun jefa iyalai da dama cikin matsanancin talauci, wanda ya tilasta musu yin rayuwa cikin matsananciyar wahala a Nijeriya.

“Ya zama wajibi shugabanninmu su farka daga barcin da suke yi, su dauki matakan da suka dace don magance musabbabin wadannan munanan abubuwan da suka faru. Wannan ba wai kawai kira ne na inganta shugabanci ba, amma kira ne na fayyacewa na kare martaba da rayuwar Dan’adam. Lokaci ya yi da shugabanninmu za su saurari kukan jama’a, su kuma ba da fifiko kan matakan da suka dace na siyasa da za su inganta rayukan al’umma maimakon tauye hakkin ‘yan Nijeriya.

“Muna kira ga gwamnati da ta aiwatar da matakan da za su hana wa ‘yan Nijeriya zama mabarata a cikin kasar nan da kuma tabbatar da tsaron lafiyar ‘yan kasa a wajen tarukan jama’a. Sake duba muggan manufofin gwamnatin Tinubu da kawo tsare-tsare masu dorewa da za su rage radadin talauci da samar da ababen more rayuwa ga al’ummarmu shi ne abin da PRP ke bukata.

“Haka nan muna ba da shawara mai karfi da al’ummar kasar nan da su yi watsi da APC da PDP, domin su ne suka haddasa mana bakin talauci da kuncin rayuwa. Shekaru 26 ya isa ya tabbatar da duk wasu alkawarin da jam’iyyun siyasar suka yi wajen kyautata rayuwal al’umma. Dole ne masu zabe su yi abu mai kyau ta yadda kuri’unsu zai sauya akalar abubuwa a kasar nan.

“Tunaninmu da addu’o’inmu sun kasance tare da iyalan da ke cikin bakin ciki a wannan mawuyacin lokaci,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Kananan Hukumomi A Zamfara Ta Gabatar Da Bitar Kasafin Kudin Kananan Hukumomi 

Next Post

Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

Related

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

5 hours ago
majalisar kasa
Tambarin Dimokuradiyya

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

6 hours ago
Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

5 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

7 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

1 week ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

1 week ago
Next Post
Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.