ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turmutsutsin Rabon Kayan Tallafi: Alama Ce Na Yadda Gwamnatin APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci – PRP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
2 years ago
PRP

Jam’iyyar PRP ta jajantawa iyalan ‘yan Nijeriya da suka mutu a turmutsitsin da ya faru a Ibadan, Abuja, da kuma Jihar Anambra, inda ta ce wannan mummunan lamari ya nuna irin talaucin da jam’iyyar APC mai mulki a karkashin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ‘yan Nijeriya a ciki bayan cire tallafin man fetur da kuma aiwatar da wasu manufofin da ba su dace ba wadanda suka yi illa ga ‘yan kasa.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Kwamared Muhammed Ishak, ya fitar wanda aka raba wa ‘yan jarida a Abuja, yayin da ta dora wa gwamnatin tarayya alhakkin wannan lamarin, ta ce ya kamata shugabanni a matakai daban-daban na gwamnati su farka daga dogon barci da suke ciki tare da dauki matakai na gaggawa don magance tushen ire-iren wadannan al’amuran da suke faruwa a kasar nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Shinkafar Kirsimeti A Kaduna
  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti

“Jam’iyyar PRP tana mika jajenta ga iyalai da al’ummomin da suka mutu a wani mummunan turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafi a Ibadan ta Jihar Oyo, da Abuja da kuma Anambra. Wadannan munanan abubuwan da suka faru, musamman a Abuja da Anambra, na nuna matukar damuwa da yanayin da ‘yan Nijeriya da suka tsinci kawunansu a cikin a gwamnatin APC.

ADVERTISEMENT

“Lamarin ya nuna yadda tsananin talauci da fatara da ke wanzuwa a cikin al’ummarmu, al’amuran da ya ta’azzara saboda rashin shugabanci na tsawon shekaru a kasar nan.

“Yayin da muke alhinin rayukan da aka rasa kan wannan lamari, dole ne mu kuma gane cewa wadannan bala’o’i na nuni ne da irin rikicin da al’umma suka tsinci kansu a ciki. Irin wannan lamari yana bukatar daukar matakin gaggawa daga wurin gwamnati a matakai daban-dabn da na al’umma gaba daya. Abubuwan da ke faruwa suna fallasa gazawar ba da fifiko ga walwala da amincin ‘yan kasa a cikin matsanancin yanayin zamantakewa da tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

“Jam’iyyar PRP ta dora wa gwamnatin tarayya da shugabancinta laifi, musamman Shugaban kasa Bola Ahmed Bola, wanda ya ingiza miliyoyin ‘yan Nijeriya ciki bakin talauci, biyo bayan cire tallafin man fetur da aiwatar da wasu manufofin da suka yi tasiri ga marasa karfi a cikinmu. Irin wadannan manufofin sun jefa iyalai da dama cikin matsanancin talauci, wanda ya tilasta musu yin rayuwa cikin matsananciyar wahala a Nijeriya.

“Ya zama wajibi shugabanninmu su farka daga barcin da suke yi, su dauki matakan da suka dace don magance musabbabin wadannan munanan abubuwan da suka faru. Wannan ba wai kawai kira ne na inganta shugabanci ba, amma kira ne na fayyacewa na kare martaba da rayuwar Dan’adam. Lokaci ya yi da shugabanninmu za su saurari kukan jama’a, su kuma ba da fifiko kan matakan da suka dace na siyasa da za su inganta rayukan al’umma maimakon tauye hakkin ‘yan Nijeriya.

“Muna kira ga gwamnati da ta aiwatar da matakan da za su hana wa ‘yan Nijeriya zama mabarata a cikin kasar nan da kuma tabbatar da tsaron lafiyar ‘yan kasa a wajen tarukan jama’a. Sake duba muggan manufofin gwamnatin Tinubu da kawo tsare-tsare masu dorewa da za su rage radadin talauci da samar da ababen more rayuwa ga al’ummarmu shi ne abin da PRP ke bukata.

“Haka nan muna ba da shawara mai karfi da al’ummar kasar nan da su yi watsi da APC da PDP, domin su ne suka haddasa mana bakin talauci da kuncin rayuwa. Shekaru 26 ya isa ya tabbatar da duk wasu alkawarin da jam’iyyun siyasar suka yi wajen kyautata rayuwal al’umma. Dole ne masu zabe su yi abu mai kyau ta yadda kuri’unsu zai sauya akalar abubuwa a kasar nan.

“Tunaninmu da addu’o’inmu sun kasance tare da iyalan da ke cikin bakin ciki a wannan mawuyacin lokaci,” in ji sanarwar.

PRP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
PRP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • Sulaiman
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.