ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turmutsutsin Rabon Kayan Tallafi: Alama Ce Na Yadda Gwamnatin APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci – PRP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
1 year ago
PRP

Jam’iyyar PRP ta jajantawa iyalan ‘yan Nijeriya da suka mutu a turmutsitsin da ya faru a Ibadan, Abuja, da kuma Jihar Anambra, inda ta ce wannan mummunan lamari ya nuna irin talaucin da jam’iyyar APC mai mulki a karkashin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ‘yan Nijeriya a ciki bayan cire tallafin man fetur da kuma aiwatar da wasu manufofin da ba su dace ba wadanda suka yi illa ga ‘yan kasa.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Kwamared Muhammed Ishak, ya fitar wanda aka raba wa ‘yan jarida a Abuja, yayin da ta dora wa gwamnatin tarayya alhakkin wannan lamarin, ta ce ya kamata shugabanni a matakai daban-daban na gwamnati su farka daga dogon barci da suke ciki tare da dauki matakai na gaggawa don magance tushen ire-iren wadannan al’amuran da suke faruwa a kasar nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Shinkafar Kirsimeti A Kaduna
  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti

“Jam’iyyar PRP tana mika jajenta ga iyalai da al’ummomin da suka mutu a wani mummunan turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafi a Ibadan ta Jihar Oyo, da Abuja da kuma Anambra. Wadannan munanan abubuwan da suka faru, musamman a Abuja da Anambra, na nuna matukar damuwa da yanayin da ‘yan Nijeriya da suka tsinci kawunansu a cikin a gwamnatin APC.

ADVERTISEMENT

“Lamarin ya nuna yadda tsananin talauci da fatara da ke wanzuwa a cikin al’ummarmu, al’amuran da ya ta’azzara saboda rashin shugabanci na tsawon shekaru a kasar nan.

“Yayin da muke alhinin rayukan da aka rasa kan wannan lamari, dole ne mu kuma gane cewa wadannan bala’o’i na nuni ne da irin rikicin da al’umma suka tsinci kansu a ciki. Irin wannan lamari yana bukatar daukar matakin gaggawa daga wurin gwamnati a matakai daban-dabn da na al’umma gaba daya. Abubuwan da ke faruwa suna fallasa gazawar ba da fifiko ga walwala da amincin ‘yan kasa a cikin matsanancin yanayin zamantakewa da tattalin arziki.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

“Jam’iyyar PRP ta dora wa gwamnatin tarayya da shugabancinta laifi, musamman Shugaban kasa Bola Ahmed Bola, wanda ya ingiza miliyoyin ‘yan Nijeriya ciki bakin talauci, biyo bayan cire tallafin man fetur da aiwatar da wasu manufofin da suka yi tasiri ga marasa karfi a cikinmu. Irin wadannan manufofin sun jefa iyalai da dama cikin matsanancin talauci, wanda ya tilasta musu yin rayuwa cikin matsananciyar wahala a Nijeriya.

“Ya zama wajibi shugabanninmu su farka daga barcin da suke yi, su dauki matakan da suka dace don magance musabbabin wadannan munanan abubuwan da suka faru. Wannan ba wai kawai kira ne na inganta shugabanci ba, amma kira ne na fayyacewa na kare martaba da rayuwar Dan’adam. Lokaci ya yi da shugabanninmu za su saurari kukan jama’a, su kuma ba da fifiko kan matakan da suka dace na siyasa da za su inganta rayukan al’umma maimakon tauye hakkin ‘yan Nijeriya.

“Muna kira ga gwamnati da ta aiwatar da matakan da za su hana wa ‘yan Nijeriya zama mabarata a cikin kasar nan da kuma tabbatar da tsaron lafiyar ‘yan kasa a wajen tarukan jama’a. Sake duba muggan manufofin gwamnatin Tinubu da kawo tsare-tsare masu dorewa da za su rage radadin talauci da samar da ababen more rayuwa ga al’ummarmu shi ne abin da PRP ke bukata.

“Haka nan muna ba da shawara mai karfi da al’ummar kasar nan da su yi watsi da APC da PDP, domin su ne suka haddasa mana bakin talauci da kuncin rayuwa. Shekaru 26 ya isa ya tabbatar da duk wasu alkawarin da jam’iyyun siyasar suka yi wajen kyautata rayuwal al’umma. Dole ne masu zabe su yi abu mai kyau ta yadda kuri’unsu zai sauya akalar abubuwa a kasar nan.

“Tunaninmu da addu’o’inmu sun kasance tare da iyalan da ke cikin bakin ciki a wannan mawuyacin lokaci,” in ji sanarwar.

PRP
Yusuf Shuaibu
+ posts Bio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye
PRP
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

PRP
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.