• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Turmutsutsin Rabon Kayan Tallafi: Alama Ce Na Yadda Gwamnatin APC Ta Jefa ‘Yan Nijeriya Cikin Talauci – PRP

by Yusuf Shuaibu and Sulaiman
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
PRP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PRP ta jajantawa iyalan ‘yan Nijeriya da suka mutu a turmutsitsin da ya faru a Ibadan, Abuja, da kuma Jihar Anambra, inda ta ce wannan mummunan lamari ya nuna irin talaucin da jam’iyyar APC mai mulki a karkashin Shugaba Bola Tinubu ta jefa ‘yan Nijeriya a ciki bayan cire tallafin man fetur da kuma aiwatar da wasu manufofin da ba su dace ba wadanda suka yi illa ga ‘yan kasa.

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun mukaddashin sakataren yada labarai na kasa na jam’iyyar, Kwamared Muhammed Ishak, ya fitar wanda aka raba wa ‘yan jarida a Abuja, yayin da ta dora wa gwamnatin tarayya alhakkin wannan lamarin, ta ce ya kamata shugabanni a matakai daban-daban na gwamnati su farka daga dogon barci da suke ciki tare da dauki matakai na gaggawa don magance tushen ire-iren wadannan al’amuran da suke faruwa a kasar nan.

  • ‘Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Shinkafar Kirsimeti A Kaduna
  • Yadda Turmutsutsin Rabon Kayan Abinci Ya Dagula Karsashin Kirsimeti

“Jam’iyyar PRP tana mika jajenta ga iyalai da al’ummomin da suka mutu a wani mummunan turmutsitsin da ya faru a lokacin rabon tallafi a Ibadan ta Jihar Oyo, da Abuja da kuma Anambra. Wadannan munanan abubuwan da suka faru, musamman a Abuja da Anambra, na nuna matukar damuwa da yanayin da ‘yan Nijeriya da suka tsinci kawunansu a cikin a gwamnatin APC.

“Lamarin ya nuna yadda tsananin talauci da fatara da ke wanzuwa a cikin al’ummarmu, al’amuran da ya ta’azzara saboda rashin shugabanci na tsawon shekaru a kasar nan.

“Yayin da muke alhinin rayukan da aka rasa kan wannan lamari, dole ne mu kuma gane cewa wadannan bala’o’i na nuni ne da irin rikicin da al’umma suka tsinci kansu a ciki. Irin wannan lamari yana bukatar daukar matakin gaggawa daga wurin gwamnati a matakai daban-dabn da na al’umma gaba daya. Abubuwan da ke faruwa suna fallasa gazawar ba da fifiko ga walwala da amincin ‘yan kasa a cikin matsanancin yanayin zamantakewa da tattalin arziki.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

“Jam’iyyar PRP ta dora wa gwamnatin tarayya da shugabancinta laifi, musamman Shugaban kasa Bola Ahmed Bola, wanda ya ingiza miliyoyin ‘yan Nijeriya ciki bakin talauci, biyo bayan cire tallafin man fetur da aiwatar da wasu manufofin da suka yi tasiri ga marasa karfi a cikinmu. Irin wadannan manufofin sun jefa iyalai da dama cikin matsanancin talauci, wanda ya tilasta musu yin rayuwa cikin matsananciyar wahala a Nijeriya.

“Ya zama wajibi shugabanninmu su farka daga barcin da suke yi, su dauki matakan da suka dace don magance musabbabin wadannan munanan abubuwan da suka faru. Wannan ba wai kawai kira ne na inganta shugabanci ba, amma kira ne na fayyacewa na kare martaba da rayuwar Dan’adam. Lokaci ya yi da shugabanninmu za su saurari kukan jama’a, su kuma ba da fifiko kan matakan da suka dace na siyasa da za su inganta rayukan al’umma maimakon tauye hakkin ‘yan Nijeriya.

“Muna kira ga gwamnati da ta aiwatar da matakan da za su hana wa ‘yan Nijeriya zama mabarata a cikin kasar nan da kuma tabbatar da tsaron lafiyar ‘yan kasa a wajen tarukan jama’a. Sake duba muggan manufofin gwamnatin Tinubu da kawo tsare-tsare masu dorewa da za su rage radadin talauci da samar da ababen more rayuwa ga al’ummarmu shi ne abin da PRP ke bukata.

“Haka nan muna ba da shawara mai karfi da al’ummar kasar nan da su yi watsi da APC da PDP, domin su ne suka haddasa mana bakin talauci da kuncin rayuwa. Shekaru 26 ya isa ya tabbatar da duk wasu alkawarin da jam’iyyun siyasar suka yi wajen kyautata rayuwal al’umma. Dole ne masu zabe su yi abu mai kyau ta yadda kuri’unsu zai sauya akalar abubuwa a kasar nan.

“Tunaninmu da addu’o’inmu sun kasance tare da iyalan da ke cikin bakin ciki a wannan mawuyacin lokaci,” in ji sanarwar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ma’aikatar Kananan Hukumomi A Zamfara Ta Gabatar Da Bitar Kasafin Kudin Kananan Hukumomi 

Next Post

Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

6 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

6 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

6 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

4 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

4 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

1 month ago
Next Post
Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

Hari Na Biyu Ba Na Jirgin Soji Ba Ne Da Ya Kashe Mutane A Sakkwato – DHQ

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana

July 10, 2025
Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita

July 10, 2025
Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

Li Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da ALLi Qiang Ya Gana Da Manyan Jami’an Masar Da AL

July 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

Ƴan Bindiga Sun Yi Wa Jami’an NSCDC Ƙwantan Ɓauna A Binuwe

July 10, 2025
Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

Yadda JKS Ta Jure Tsawon Tarihin Gwagwarmaya Da Cimma Nasarori

July 10, 2025
An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano

July 10, 2025
Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

Xi Jinping Ya Aike Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adam

July 10, 2025
Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

Majalisar Ta Kwace Shugabacin Kwamitin Da Natasha Ke Jagoranta

July 10, 2025
An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing

July 10, 2025
Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

Shiri Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Tabbatar Da Ci Gaban Kasar Sin

July 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.