• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Akwa Ibom ta gurfanar da wani mutum mai suna Aniekan James bisa zarginsa da kashe dansa guda daya tilo da Allah ya ba shi, Odudu James, mai shekara 35 a duniya.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ya gurfanar wanda ake zargin da wasu 268 da aka kama bisa zargin aikata laifuka daban-daban, ana kuma zargin Aniekan da kashe wasu da dama a Legas da Jihar Abia.

  • Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu
  • Ziyarar Firaministan Kasar Tsibiran Solomon A Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana Ga Kasar

Kwamishinan ya ce, jami’an hukumar na caji ofis din Ukanafun ne suka cafke wanda ake zargin a ranar 16 ga watan Yunin 2023.

 Ya ce, “A ranar 16 ga watan Yunin 2023 ne jami’an caji ofis din Ukanafun suka cafke wani mutum Aniekan James na kauyen Ikot Ndot da ke karamar hukumar Ukanafun bisa laifin harbe dansa mai shekara 35, Odudu James, sakamakon cacar baki da ta shiga tsakaninsu. Ana zargin wanda aka kama din da aikata laifukan kisan mutane da dama a jihohin Legas da Abia.”

Kazalika, kwamishinan ya kuma gurfanar da wani bisa zargin yin garkuwa da mukaddashin shugaban wata jami’a mai zaman kanta da aka sace a lokacin da yake hanyarsa ta komawa gida.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Ya ce, sauran miliyan biyu na kudin fansa da mota kirar Toyota Corolla da aka yi amfani da su wajen aikata laifin an kwato su yayin da shugaban makarantar ya koma cikin iyalansa.

Ya ce an yi garkuwa da mataimakin shugaban jami’ar ne a ranar 14 ga watan Afrilun 2023 a lokacin da ke hanyarsa ta komawa gida. Amma bayan kwana biyu da sace shi, rundunar ra kama wani mai suna Prince Thursday Okon wani tsohon ma’aikacin babban malamin din ne da zargin shi ne ya sace shugaban makarantar.

“An kori Okon daga aiki bisa zargin aikata manyan laifuka. An kama shi ne tare da abokan aikata laifukansu biyu, Sabiour Sunday Luke da Richard Friday, dukkaninsu ‘yan kauyen Ikot Ebam da ke karamar hukumar Mkpan Enin.”

Har-ila-yau, an gurfanar da wani Edu Ime bisa zarginsa da zama mamba na kungiyar asiri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cacar-bakiDaKisaMahaifi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu

Next Post

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.