• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Uba Ya Hallaka Dansa Daya Tilo Kan Cacar-baki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar ‘yansandan Jihar Akwa Ibom ta gurfanar da wani mutum mai suna Aniekan James bisa zarginsa da kashe dansa guda daya tilo da Allah ya ba shi, Odudu James, mai shekara 35 a duniya.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, Olatoye Durosinmi, shi ne ya shaida hakan a lokacin da ya gurfanar wanda ake zargin da wasu 268 da aka kama bisa zargin aikata laifuka daban-daban, ana kuma zargin Aniekan da kashe wasu da dama a Legas da Jihar Abia.

  • Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu
  • Ziyarar Firaministan Kasar Tsibiran Solomon A Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana Ga Kasar

Kwamishinan ya ce, jami’an hukumar na caji ofis din Ukanafun ne suka cafke wanda ake zargin a ranar 16 ga watan Yunin 2023.

 Ya ce, “A ranar 16 ga watan Yunin 2023 ne jami’an caji ofis din Ukanafun suka cafke wani mutum Aniekan James na kauyen Ikot Ndot da ke karamar hukumar Ukanafun bisa laifin harbe dansa mai shekara 35, Odudu James, sakamakon cacar baki da ta shiga tsakaninsu. Ana zargin wanda aka kama din da aikata laifukan kisan mutane da dama a jihohin Legas da Abia.”

Kazalika, kwamishinan ya kuma gurfanar da wani bisa zargin yin garkuwa da mukaddashin shugaban wata jami’a mai zaman kanta da aka sace a lokacin da yake hanyarsa ta komawa gida.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Ya ce, sauran miliyan biyu na kudin fansa da mota kirar Toyota Corolla da aka yi amfani da su wajen aikata laifin an kwato su yayin da shugaban makarantar ya koma cikin iyalansa.

Ya ce an yi garkuwa da mataimakin shugaban jami’ar ne a ranar 14 ga watan Afrilun 2023 a lokacin da ke hanyarsa ta komawa gida. Amma bayan kwana biyu da sace shi, rundunar ra kama wani mai suna Prince Thursday Okon wani tsohon ma’aikacin babban malamin din ne da zargin shi ne ya sace shugaban makarantar.

“An kori Okon daga aiki bisa zargin aikata manyan laifuka. An kama shi ne tare da abokan aikata laifukansu biyu, Sabiour Sunday Luke da Richard Friday, dukkaninsu ‘yan kauyen Ikot Ebam da ke karamar hukumar Mkpan Enin.”

Har-ila-yau, an gurfanar da wani Edu Ime bisa zarginsa da zama mamba na kungiyar asiri.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cacar-bakiDaKisaMahaifi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kyan Wayewar Kai Na Cikin Bambance-Bambancen Dake Akwai Tsakaninsu

Next Post

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

7 days ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 week ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

Barawo Ya Gamu Da Ajalinsa Garin Sata A Taransifoma

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.