• English
  • Business News
Tuesday, May 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi da su fara cire harajin tsaro na intanet kan kowani hada-hadar banki da ‘yan Nijeriya za su yi.

A cewar sanarwar da babban bankin ya fitar, za a fara biyan sabon harajin ne nan da mako biyu masu zuwa.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Ga wasu abubuwan da ya dace ku sani kan harajin tsaro na intanet da ‘yan Nijeriya za su dunga biya kamar yadda CBN ya umarta.

Za a rika cire harajin kaso 0.5 cikin dari, kwatankwacin rabin kaso, zai kasance kan dukkanin hada-hadar kudi da aka yi ta yanar gizo ne. Duk kwastoman da ya yi hada-hadar banki ta intanet za a caje shi wannan sabon harajin, kuma bankin da yake ne za su cire kason kai tsaye. Za a sanar da kwastoma ta cikin jadawalin asusun ajiyarsa na cewa an cire wannan kudin.

Haka kuma, bayan bankuna sun cire wannan kudin harajin za su shigar da kudin kai tsaye zuwa asusun harajin tsaron intanet na kasa da ke ofishin babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro. Za a fara aiwatar da cire kudin ne nan da mako biyu daga ranar da CBN ta sake sanarwa, ranar 6 ga watan Mayu, kuma bankuna za su shigar da kudin zuwa asusun NCF ne a dunkule.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Sannan bankuna za su amfani da tsarin da ke cire harajin da shigar da shi asusun da aka ware. Dukkanin bankin da ya kasa shigar da wannan harajin akwai cin tara da za a yi masa da suka hada da cire kaso biyu cikin dari na kason wannan bankin na shekara-shekara.

Sai dai kum, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi watsi da wannan umurnin na babban banki kan cire kasha 05 na harajin tsaro ga kowani hada-hadar kudi ta intanet.

Shugaban NLC, Joe Ajaero shi ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Abuja.

Ajaero ya dai yi watsi da sanarwar CBN kan wannan haraji da zai fara aiki nan da wakonni biyu.

A cewar Ajaero, NLC ta yi Allah wadai da wannan mataki tare da kiran gwamnatin tarayya ta gaggauta janye matakin.

Ya ce kakaba wannan harajin zai tagayyara ‘yan kara fiye da halin da ake ciki a yanzu.

Ita kungiyar kokarin tabbatar da adalci ta SERAP ta nuna adawarta da sabon harajin na tsaron intanet.

Kungiyar ta bukaci Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu da ya bai wa Babban Bankin Nijeriya umarnin soke harajin kafin nan da awa 48 kasancewar ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da kuma walwalar al’umma.

Wannan haraji zai zamo doriya ne a kan jerin haraje-haraje da al’ummar Nijeriya ke biya wadanda babban bankin kasar ya kakaba musu.

Cikin su akwai harajin kula da katin ATM, da kula da asusun ajiya, harajin gwamnati, cajin tura kudi daga wani banki zuwa wani da kuma harajin tura kudi ta laturoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BakunaCBNHarajiIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

Next Post

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

Related

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

1 hour ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

3 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

4 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

7 hours ago
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa
Labarai

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

9 hours ago
Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano
Labarai

Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe ÆŠakunan Kwanan ÆŠalibai Saboda Aikata Rashin ÆŠa’a A Kano

10 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

Xi Jinping Ya Halarci Bikin Bude Taro Na 4 Na Ministocin Dandalin CCF 

May 13, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

Kasar Sin Ta Fitar Da Tambarin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Murkushe Harin Japan

May 13, 2025
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

May 13, 2025
Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

Rikicin Ribas: Fubara Ya Ce Ya San Yadda Zai Magance Matsalar, Ya GargaÉ—i Magoya Bayansa

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.