• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi da su fara cire harajin tsaro na intanet kan kowani hada-hadar banki da ‘yan Nijeriya za su yi.

A cewar sanarwar da babban bankin ya fitar, za a fara biyan sabon harajin ne nan da mako biyu masu zuwa.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Ga wasu abubuwan da ya dace ku sani kan harajin tsaro na intanet da ‘yan Nijeriya za su dunga biya kamar yadda CBN ya umarta.

Za a rika cire harajin kaso 0.5 cikin dari, kwatankwacin rabin kaso, zai kasance kan dukkanin hada-hadar kudi da aka yi ta yanar gizo ne. Duk kwastoman da ya yi hada-hadar banki ta intanet za a caje shi wannan sabon harajin, kuma bankin da yake ne za su cire kason kai tsaye. Za a sanar da kwastoma ta cikin jadawalin asusun ajiyarsa na cewa an cire wannan kudin.

Haka kuma, bayan bankuna sun cire wannan kudin harajin za su shigar da kudin kai tsaye zuwa asusun harajin tsaron intanet na kasa da ke ofishin babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro. Za a fara aiwatar da cire kudin ne nan da mako biyu daga ranar da CBN ta sake sanarwa, ranar 6 ga watan Mayu, kuma bankuna za su shigar da kudin zuwa asusun NCF ne a dunkule.

Labarai Masu Nasaba

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

Sannan bankuna za su amfani da tsarin da ke cire harajin da shigar da shi asusun da aka ware. Dukkanin bankin da ya kasa shigar da wannan harajin akwai cin tara da za a yi masa da suka hada da cire kaso biyu cikin dari na kason wannan bankin na shekara-shekara.

Sai dai kum, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi watsi da wannan umurnin na babban banki kan cire kasha 05 na harajin tsaro ga kowani hada-hadar kudi ta intanet.

Shugaban NLC, Joe Ajaero shi ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Abuja.

Ajaero ya dai yi watsi da sanarwar CBN kan wannan haraji da zai fara aiki nan da wakonni biyu.

A cewar Ajaero, NLC ta yi Allah wadai da wannan mataki tare da kiran gwamnatin tarayya ta gaggauta janye matakin.

Ya ce kakaba wannan harajin zai tagayyara ‘yan kara fiye da halin da ake ciki a yanzu.

Ita kungiyar kokarin tabbatar da adalci ta SERAP ta nuna adawarta da sabon harajin na tsaron intanet.

Kungiyar ta bukaci Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu da ya bai wa Babban Bankin Nijeriya umarnin soke harajin kafin nan da awa 48 kasancewar ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da kuma walwalar al’umma.

Wannan haraji zai zamo doriya ne a kan jerin haraje-haraje da al’ummar Nijeriya ke biya wadanda babban bankin kasar ya kakaba musu.

Cikin su akwai harajin kula da katin ATM, da kula da asusun ajiya, harajin gwamnati, cajin tura kudi daga wani banki zuwa wani da kuma harajin tura kudi ta laturoni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BakunaCBNHarajiIntanet
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mukalar Shugaba Xi: Hakika Kasar Sin Ba Ta Yi Wa Duniya Rowar Kaifin Basirarta Ba

Next Post

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

Related

Kawayen amarya
Labarai

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

41 minutes ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

3 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

5 hours ago
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

14 hours ago
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Labarai

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

14 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

15 hours ago
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da ÆŠumi-É—umi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake ÆŠage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.