ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Umarnin CBN Na Cire Harajin Tsaron Intanet Ya Tayar Da Kura

by Khalid Idris Doya
2 years ago
CBN

Babban bankin Nijeriya (CBN) ya umarci bankuna da sauran cibiyoyin hada-hadar kudi da su fara cire harajin tsaro na intanet kan kowani hada-hadar banki da ‘yan Nijeriya za su yi.

A cewar sanarwar da babban bankin ya fitar, za a fara biyan sabon harajin ne nan da mako biyu masu zuwa.

  • Majalisar Wakilai Ta Umarci CBN Ya Dakatar Da Harajin Tsaron Yanar Gizo
  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa

Ga wasu abubuwan da ya dace ku sani kan harajin tsaro na intanet da ‘yan Nijeriya za su dunga biya kamar yadda CBN ya umarta.

ADVERTISEMENT

Za a rika cire harajin kaso 0.5 cikin dari, kwatankwacin rabin kaso, zai kasance kan dukkanin hada-hadar kudi da aka yi ta yanar gizo ne. Duk kwastoman da ya yi hada-hadar banki ta intanet za a caje shi wannan sabon harajin, kuma bankin da yake ne za su cire kason kai tsaye. Za a sanar da kwastoma ta cikin jadawalin asusun ajiyarsa na cewa an cire wannan kudin.

Haka kuma, bayan bankuna sun cire wannan kudin harajin za su shigar da kudin kai tsaye zuwa asusun harajin tsaron intanet na kasa da ke ofishin babban mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro. Za a fara aiwatar da cire kudin ne nan da mako biyu daga ranar da CBN ta sake sanarwa, ranar 6 ga watan Mayu, kuma bankuna za su shigar da kudin zuwa asusun NCF ne a dunkule.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Sannan bankuna za su amfani da tsarin da ke cire harajin da shigar da shi asusun da aka ware. Dukkanin bankin da ya kasa shigar da wannan harajin akwai cin tara da za a yi masa da suka hada da cire kaso biyu cikin dari na kason wannan bankin na shekara-shekara.

Sai dai kum, kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC) ta yi watsi da wannan umurnin na babban banki kan cire kasha 05 na harajin tsaro ga kowani hada-hadar kudi ta intanet.

Shugaban NLC, Joe Ajaero shi ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a Abuja.

Ajaero ya dai yi watsi da sanarwar CBN kan wannan haraji da zai fara aiki nan da wakonni biyu.

A cewar Ajaero, NLC ta yi Allah wadai da wannan mataki tare da kiran gwamnatin tarayya ta gaggauta janye matakin.

Ya ce kakaba wannan harajin zai tagayyara ‘yan kara fiye da halin da ake ciki a yanzu.

Ita kungiyar kokarin tabbatar da adalci ta SERAP ta nuna adawarta da sabon harajin na tsaron intanet.

Kungiyar ta bukaci Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu da ya bai wa Babban Bankin Nijeriya umarnin soke harajin kafin nan da awa 48 kasancewar ya saba wa kundin tsarin mulkin Nijeriya da kuma walwalar al’umma.

Wannan haraji zai zamo doriya ne a kan jerin haraje-haraje da al’ummar Nijeriya ke biya wadanda babban bankin kasar ya kakaba musu.

Cikin su akwai harajin kula da katin ATM, da kula da asusun ajiya, harajin gwamnati, cajin tura kudi daga wani banki zuwa wani da kuma harajin tura kudi ta laturoni.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
Next Post
‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.