ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Lantarki

‘Yan Nijeriya sun yi fatali da shirin hukumar kula da harkokin wutar lantarki (NERC) na rage kudin wutar lantarki da suke yi a ajin A wato ‘yan ‘Band A’ daga kan naira 225 zuwa naira 206.8 kan wutan da suka sha na sa’a guda.

Kungiyar Kwadago na NLC da TUC da kungiyar kwastomomin da ke amfani da wutar lantarki da kungiyoyin farafen hula sun shaida wa jaridar Punch bukatarsu na a gaggauwa ta sake nazari kan karin kudin wutar lantarki.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Tsaron Yanar Gizo: TUC Ta Yi Barazanar Shiga Zanga-zanga A Nijeriya

Sanarwar sabon farin wutar da NERC ta yi na zuwa ne kwanaki 33 bayan da ta tsula karin farashin ga ‘yan rukunin ‘A’ daga kan naira 68 na kudin wuta da suke sha a sa’a guda zuwa naira 225, lamarin da ke nuni da cewa an kara kudin wuta da kaso 240.

ADVERTISEMENT

Kan karin kudin, gwamnatin tarayya ta ce hakan zai ba ta damar samun rarar naira tiriliyan 1.5.

Bugu da kari, majalisar wakilai, kungiyoyin kwadago da na lauyoyi sun yi tir da karin kudin wutar lantarki da ya shafi sama da kwastomomi miliyan 1.9.

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

Majalisar wakilai ta yi kira ga NERC da ta janye shirinta na karin kudin wutar lantarki a fadin kasa, yayin da kungiyar kwadago ta bayar da wa’adin mako biyu da a sake nazarin karin kudin wutar lantarki cikin gaggawa.

Sai dai, ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya dage kan dole fa ‘yan kasa su amince da karin kudin, yana mai cewa idan zuwa nan da wata uku ba a aiwatar da karin farashin ba, to kuwa al’umman Nijeriya za su rasa wutan ma baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan lamarin, mataimakin shugaban kungiyar TUC, Tommy Etim, ya ce, “Ba zai yuwu a amince da hakan ba. Gaba daya muna son a janye batun karin kudin wutar nan.”

Shi ma ma’ajin kungiyar NLC, Hakeem Ambali, cewa ya yi, “Wannan lamarin ya kasance abun damuwa matuka ga kungiyar kwadago, muddin ba wai samun karuwar wuta aka yi ba, kowani irin karin kudin da aka yi na wuta ba abun lamunta ba ne.”

Shugaban kungiyar NACCIMA, Dele Oye ya ce kamfanonin rarraba wutar lantarki a Nijeriya ba su da dalilin da za su buga karji su yi karin kudin wutan lantarki. Ya ce akwai bukatar masu ruwa da tsaki su sa baki wajen ganin an janye batun baki daya.

Shugaban NACCIMA ya ce muddin ba a samu ra’ayin masu ruwa da suka hada da kamfanoni, ‘yan kasuwa, masu amfani da wuta da kungiyoyin fararen huda ba wajen tattauna yadda za a yi karin kudin.

Lantarki
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221
Labarai

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Next Post
Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (1)

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (1)

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.