ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Yi Fatali Da Ragin Kudin Wutar Lantarki

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Lantarki

‘Yan Nijeriya sun yi fatali da shirin hukumar kula da harkokin wutar lantarki (NERC) na rage kudin wutar lantarki da suke yi a ajin A wato ‘yan ‘Band A’ daga kan naira 225 zuwa naira 206.8 kan wutan da suka sha na sa’a guda.

Kungiyar Kwadago na NLC da TUC da kungiyar kwastomomin da ke amfani da wutar lantarki da kungiyoyin farafen hula sun shaida wa jaridar Punch bukatarsu na a gaggauwa ta sake nazari kan karin kudin wutar lantarki.

  • Almundahana: Kotu Ta Bayar Da Belin Hadi Sirika Da ‘Yarsa
  • Tsaron Yanar Gizo: TUC Ta Yi Barazanar Shiga Zanga-zanga A Nijeriya

Sanarwar sabon farin wutar da NERC ta yi na zuwa ne kwanaki 33 bayan da ta tsula karin farashin ga ‘yan rukunin ‘A’ daga kan naira 68 na kudin wuta da suke sha a sa’a guda zuwa naira 225, lamarin da ke nuni da cewa an kara kudin wuta da kaso 240.

ADVERTISEMENT

Kan karin kudin, gwamnatin tarayya ta ce hakan zai ba ta damar samun rarar naira tiriliyan 1.5.

Bugu da kari, majalisar wakilai, kungiyoyin kwadago da na lauyoyi sun yi tir da karin kudin wutar lantarki da ya shafi sama da kwastomomi miliyan 1.9.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Majalisar wakilai ta yi kira ga NERC da ta janye shirinta na karin kudin wutar lantarki a fadin kasa, yayin da kungiyar kwadago ta bayar da wa’adin mako biyu da a sake nazarin karin kudin wutar lantarki cikin gaggawa.

Sai dai, ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu, ya dage kan dole fa ‘yan kasa su amince da karin kudin, yana mai cewa idan zuwa nan da wata uku ba a aiwatar da karin farashin ba, to kuwa al’umman Nijeriya za su rasa wutan ma baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan lamarin, mataimakin shugaban kungiyar TUC, Tommy Etim, ya ce, “Ba zai yuwu a amince da hakan ba. Gaba daya muna son a janye batun karin kudin wutar nan.”

Shi ma ma’ajin kungiyar NLC, Hakeem Ambali, cewa ya yi, “Wannan lamarin ya kasance abun damuwa matuka ga kungiyar kwadago, muddin ba wai samun karuwar wuta aka yi ba, kowani irin karin kudin da aka yi na wuta ba abun lamunta ba ne.”

Shugaban kungiyar NACCIMA, Dele Oye ya ce kamfanonin rarraba wutar lantarki a Nijeriya ba su da dalilin da za su buga karji su yi karin kudin wutan lantarki. Ya ce akwai bukatar masu ruwa da tsaki su sa baki wajen ganin an janye batun baki daya.

Shugaban NACCIMA ya ce muddin ba a samu ra’ayin masu ruwa da suka hada da kamfanoni, ‘yan kasuwa, masu amfani da wuta da kungiyoyin fararen huda ba wajen tattauna yadda za a yi karin kudin.

Lantarki
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (1)

Falalar Goman Farko Na Watan Zulhajji (1)

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.