• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
in Labarai
0
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Kula da Kananan Yarana Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya yi gargadi kan yiwuwar bullar matsalolin ayyukan jin kai a Nijeriya, sakamakon wawakeken gibin kudaden tallafi da ke barazana ga muhimman ayyuka na lafiya, abinci mai gina jiki, ilimi da kuma samar da ruwa a fadin kasar.

Da yake magana a Maiduguri a ranar Litinin yayin bikin tunawa da Ranar Jin Kai ta Duniya ta 2025, Shugaban Ofishin UNICEF na Maiduguri, Francis Butichi, ya bayyana cewa hukumar ta samu Dala miliyan 95 kacal daga cikin Dala miliyan 255 da ake bukata don gudanar da ayyukan bana, abin da ya bar gibin Dala miliyan 160 (Naira biliyan 240) kashi 67 cikin dari na gibin kudi.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

“Muna sane da yankewar kudaden tallafi na duniya da yake barazana ga ayyukan jin kai a fadin duniya. Tasirinsa kuwa yana da matukar muni a matakin cikin gida, inda rikice-rikice, canjin yanayi da barkewar cututtuka ke maimaituwa,” in ji Butichi.

Duk da kalubalen da ake fuskanta, UNICEF ta ce ta kai wa sama da mutum miliyan 1.3 hidimar kiwon lafiya, ta warkar da yara 340,000 da suka kamu da matsanancin karancin abinci mai gina jiki, ta samar da ruwan sha mai tsafta ga mutane 185,000, tare da saka yara 500,000 ‘yan gudun hijira a makarantu.

Butichi ya roki bangaren masu zaman kansu, gwamnati da masu bayar da tallafi da su ci gaba da karin goyon baya ga hukumomin kananan hukumomi da kungiyoyin fararen hula da ke bayar da ayyuka a sahun gaba.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

“Bai kamata a dakatar da hidimomin ceto rayuka na abinci mai gina jiki, allurar rigakafi, kiwon lafiya da kariya ga al’ummomin da rikici, ambaliyar ruwa da kuma hijira suka shafa ba,” ya jaddada.

Jihohin Arewa na shirin fuskantar wannan kalubale

A halin yanzu, wasu gwamnatocin jihohin Arewa sun ce suna daukar matakai don rage illolin karancin kudaden da ke tafe.

A Gombe

Daraktan Yada Labarai na Fadar Gwamnati, Ismaila Misilli, ya shaida wa The PUNCH cewa jihar ta riga ta hango kalubalen kuma ta tanadi kasafin kudi don tallafa wa al’umma masu rauni.

“Mun ware kasafin kudi na musamman don kiwon lafiya, ilimi, ci gaban dan’Adam da kuma yaran da ba sa zuwa makaranta. Don haka, akwai tsari a kan wannan hanya.”

Jihar Kebbi

Ita ma ta bayyana aniyarta na ci gaba da tallafa wa shirye-shiryen UNICEF.

Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Alhaji Ahmed Idris, ya ce jihar ta riga ta biya kudin hadin gwiwa kuma ba za ta yi sakaci ba.

Sakkwato

Haka kuma, wani babban jami’i a Sokoto ya tabbatar da cewa Gwamna Ahmed Aliyu kwanan nan ya amince da Naira miliyan 500 a matsayin kudin hadin guiwa don ayyukan UNICEF a fannoni muhimmai, tare da ware karin kudi don aiwatar da ayyuka.

Jigawa

A Jigawa kuwa, jami’an gwamnati sun amince cewa gibin kudi zai iya yin mummunan tasiri ga isar da muhimman ayyukan kiwon lafiya kamar abinci mai gina jiki, rigakafi da kuma samun ruwan sha mai tsabta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: UNICEF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Next Post

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Related

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

10 minutes ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

2 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

4 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

5 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

9 hours ago
Next Post
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

LABARAI MASU NASABA

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.