• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano

by Bello Hamza
1 day ago
in Labarai
0
VFS Ta Ƙaddamar Da Cibiyar Yin Biza Zuwa Birtaniya A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani mataki na sauƙaƙa samun damar yin biza na Birtaniya ga matafiya daga Arewacin Nijeriya, kamfanin VFS Global tare da haɗin gwiwar Hukumar Biza da Shige da Fice ta Birtaniya (UKVI) sun kaddamar da sabuwar Cibiyar Aikace-aikacen biza ta Musamman a Kano.

An buɗe cibiyar ne a Bristol Palace Hotel, lamba 54–56 titin Guda Abdullahi, inda za ta bai wa mazauna Kano da sauran yankunan Arewa damar gabatar da buƙatun biza da yin rijista cikin sauƙi, musamman kafin lokacin tafiye-tafiyen bazara da ke tunkarowa.

  • Kasar Sin Ta Ba Baki Masu Yawon Bude Ido Dake Cikin Jiragen Ruwa Na Nishadi Izinin Shiga Kasar Ba Tare Da Visa Ba 
  • Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Hajiya Gill Lever, wadda ke matsayin Chargée d’Affaires a ofishin jakadancin Birtaniya da ke Abuja, ta bayyana jin daɗinta game da faɗaɗa ayyukan bada biza a Nijeriya.

“Ina farin cikin tabbatar da ci gaba da faɗaɗa ayyukan bada biza na Birtaniya a faɗin Nijeriya, da kaddamar da sabuwar Cibiyar Aikace-aikace ta Musamman ta VFS a Kano,” in ji ta. “Kano da sauran Arewacin Nijeriya na da matuƙar muhimmanci a dangantakar Birtaniya da Nijeriya. Sabuwar cibiyar za ta taimaka wajen sauƙaƙa wa mutane samun ingantaccen sabis na biza a kusa da inda suke.”

Ta kuma bayyana cewa Nijeriya na daga cikin ƙasashen da ke da yawan masu ziyartar Birtaniya daga nahiyar Afirka, inda take cikin ƙasashe huɗu mafi yawan masu nema, kuma tana da kusan kashi 6 cikin 100 na adadin aikace-aikacen biza a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Wannan cibiyar da aka buɗe a Kano ita ce ta uku da VFS Global ta kaddamar a cikin ‘yan watannin baya a Nijeriya, bayan buɗe makamantansu a Enugu da Port Harcourt. Cibiyoyin na ƙara wa waɗanda ke Abuja da Legas (Ikeja da Victoria Island), waɗanda ke aiki tun daga Nuwamba 2024.

Mista Alok Singhal, shugaban yankin hamadar nahiyar Afirka na VFS Global, ya jaddada aniyar kamfanin na kawo sauƙi ga abokan cinikinsu.

“Muna farin ciki da ƙara yawan wuraren da za a iya samun sabis na biza cikin sauƙi ga ‘yan Nijeriya, musamman da buɗe sabuwar cibiyar mu ta Musamman a Kano,” in ji shi. “Yayin da buƙatar tafiya zuwa Birtaniya ke ƙaruwa, burinmu shi ne mu samar da irin ingantaccen sabis, sauƙi da jin daɗi da muke bayarwa a Abuja da Legas a nan Kano.”

Sabuwar cibiyar da ke Kano na bayar da sabis na musamman da suka haɗa da taimako wajen lodin takardu, sanarwa kai-tsaye kan matsayin aikace-aikace, da isar da takardu ta hanyar sakonni. Haka kuma, abokan ciniki za su iya amfani da sabis ɗin “Ajiye Fasfo ɗina Bayan sa hannu”, wanda ke ba su damar ci gaba da amfani da fasfo ɗinsu bayan rijistar, sannan su miƙa shi daga baya idan an yanke hukunci.

Kamfanin VFS Global wanda ke aiki da ‘UK Visas and Immigration’ tun shekarar 2003, ya soma bayar da sabis a ƙasashe 58. A shekarar 2023, an sake ba su kwangilar bayar da sabis a ƙasashe 142, alamar yarda da ƙwarewarsu a fannin.

Ga mazauna Kano da sauran yankunan Arewacin Nijeriya, wannan sabuwar cibiyar na nufin ƙarin sauƙi, jin daɗi da saurin aiki – wanda zai ƙarfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da Birtaniya a fannonin kasuwanci, yawon buɗe ido, ilimi da musayar al’adu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BirtaniyaBizakanoVisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Next Post

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Related

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu
Manyan Labarai

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

25 minutes ago
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi
Labarai

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

9 hours ago
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika
Labarai

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

10 hours ago
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde
Labarai

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

12 hours ago
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025
Labarai

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

13 hours ago
Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

16 hours ago
Next Post
Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ƙungiyar Buzaye Ta Yi Wa Nijeriya Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

LABARAI MASU NASABA

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

Za A Ci Gaba Da Zaman Makokin Buhari A Abuja – Garba Shehu

July 17, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.