• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Ya Ce A Cikin Kananan Hukumomin Jihar 17, 4 Kacal Suke Da Banki

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Labarai
0
Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya bukaci Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kara wa al’ummar jihar Yobe wa’adi na daban, da zai bayar da damar canza tsoffin takardun kudadensu, sabanin 31 ga watan Janairun da ya saka da farko.

Gwamnan ya bayyana hakan a sanarwar manema labaru, ranar Lahadi, mai dauke da sa-hannun Daraka Janar kan hulda da yan jaridu da Kafafen yada labaru, Mamman Mohammed, inda ya ce Gwamna Buni ya bayyana cewa neman ƙarin wa’adin ya zama dole sakamakon yadda jihar ke fama da karancin bankuna.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kananan hukumomi hudu ne kacal cikin 17, a fadin jihar suke da bankuna, al’amarin da ya ce zai yi wahala mutane su samu damar canja kudaden su a kwanaki 13 da suka rage a wa’adin da Babban Bankin Nijeriya ya gindaya.

“Sannan kuma wasu daga cikin bankunan da suke da rassa a wasu kananan hukumomin, dole ya sa sun rufe sakamakon rikicin Boko Haram da ya yi kamari, kuma har yanzu basu sake bude su ba a fadin jihar.”

“Saboda haka muna kyautata zaton CBN zai kula wajen bai wa irin wadannan wurare kulawa ta musamman sakamakon bukatu na musamman, domin kaucewa jawo asarar kudaden jama’a.”

Labarai Masu Nasaba

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

“Kuma muna kira ga CBN da sauran bankunan Kasuwanci su kalli wannan bukata ta jama’a cikin gaggawa wajen nemawa al’umma mafita tare da dakile halin fargaban da ake ciki.”

“A matsayinsa na mai sanya ido, yana da kyau Babban Bankin Nijeriya ya tabbatar cewa bankunan Kasuwanci sun bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin saboda a halin yanzu zaman lafiya ya samu a fadin jihar Yobe.” In ji Gwamna.

  • Naja’atu Ta Yi Murabus Daga Kwamitin Yakin Zaben Tinubu, Ta Fice Daga APC

 

Bugu da kari, Gwamna Buni ya kara da cewa, ci gaban da ake samu ta fannin tsaro a jihar Yobe da Arewa Maso Gabas baki daya, babu wata fargabar da za ta hana bankuna su sake bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin da manyan garuruwa.

Har ila yau, Gwamna Buni ya sake nanata cewa, akwai fargaba matikar ba a dauki matakin gaggawa ba, saboda ko shakka babu jama’a da dama za su fuskanci barazanar karayar tattalin arziki, da dalilin canjin kudin.

  • https://leadership.ng/cbn-warns-against-rejection-of-old-naira-notes/

 

“Sannan a matsayinmu na gwamnati, wajibi ne mu yi dogon nazari don kaucewa kalubalen da zai jawo, wanda lalle akwai bukatar CBN, Babban Bankin Nijeriya ya dubi lamarin nan tare da daukar matakan da suka dace wajen shawo kan matsalar.” In ji Gwamna Buni.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

Next Post

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

Related

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

1 hour ago
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro
Tsaro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

3 hours ago
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu
Labarai

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

4 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

6 hours ago
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

8 hours ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

9 hours ago
Next Post
An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.