• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Ya Ce A Cikin Kananan Hukumomin Jihar 17, 4 Kacal Suke Da Banki

by Muhammad Maitela
3 years ago
cbn

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya bukaci Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kara wa al’ummar jihar Yobe wa’adi na daban, da zai bayar da damar canza tsoffin takardun kudadensu, sabanin 31 ga watan Janairun da ya saka da farko.

Gwamnan ya bayyana hakan a sanarwar manema labaru, ranar Lahadi, mai dauke da sa-hannun Daraka Janar kan hulda da yan jaridu da Kafafen yada labaru, Mamman Mohammed, inda ya ce Gwamna Buni ya bayyana cewa neman ƙarin wa’adin ya zama dole sakamakon yadda jihar ke fama da karancin bankuna.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kananan hukumomi hudu ne kacal cikin 17, a fadin jihar suke da bankuna, al’amarin da ya ce zai yi wahala mutane su samu damar canja kudaden su a kwanaki 13 da suka rage a wa’adin da Babban Bankin Nijeriya ya gindaya.

“Sannan kuma wasu daga cikin bankunan da suke da rassa a wasu kananan hukumomin, dole ya sa sun rufe sakamakon rikicin Boko Haram da ya yi kamari, kuma har yanzu basu sake bude su ba a fadin jihar.”

“Saboda haka muna kyautata zaton CBN zai kula wajen bai wa irin wadannan wurare kulawa ta musamman sakamakon bukatu na musamman, domin kaucewa jawo asarar kudaden jama’a.”

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

Jerin Gwarazan Taurarinmu

“Kuma muna kira ga CBN da sauran bankunan Kasuwanci su kalli wannan bukata ta jama’a cikin gaggawa wajen nemawa al’umma mafita tare da dakile halin fargaban da ake ciki.”

“A matsayinsa na mai sanya ido, yana da kyau Babban Bankin Nijeriya ya tabbatar cewa bankunan Kasuwanci sun bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin saboda a halin yanzu zaman lafiya ya samu a fadin jihar Yobe.” In ji Gwamna.

  • Naja’atu Ta Yi Murabus Daga Kwamitin Yakin Zaben Tinubu, Ta Fice Daga APC

 

Bugu da kari, Gwamna Buni ya kara da cewa, ci gaban da ake samu ta fannin tsaro a jihar Yobe da Arewa Maso Gabas baki daya, babu wata fargabar da za ta hana bankuna su sake bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin da manyan garuruwa.

Har ila yau, Gwamna Buni ya sake nanata cewa, akwai fargaba matikar ba a dauki matakin gaggawa ba, saboda ko shakka babu jama’a da dama za su fuskanci barazanar karayar tattalin arziki, da dalilin canjin kudin.

  • https://leadership.ng/cbn-warns-against-rejection-of-old-naira-notes/

 

“Sannan a matsayinmu na gwamnati, wajibi ne mu yi dogon nazari don kaucewa kalubalen da zai jawo, wanda lalle akwai bukatar CBN, Babban Bankin Nijeriya ya dubi lamarin nan tare da daukar matakan da suka dace wajen shawo kan matsalar.” In ji Gwamna Buni.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
Manyan Labarai

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu
Manyan Labarai

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Manyan Labarai

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Next Post
An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025
Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

October 31, 2025
Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.