• English
  • Business News
Tuesday, June 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
in Wasanni
0
Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu za a iya cewa wasanni za su kankama bayan da tun a ranar Juma’a, 5 ga watan Agustan 2022 aka fara buga wasannin gasar Premier League ta bana, kakar wasa ta 2022 zuwa 2023.

Idan mai karatu bai manta ba, a kakar da ta gabata kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ce ta lashe gasar, kuma biyu a jere da ta lashe wato a 2020 da 2021 da kuma ta 2021 da 2022 a karkashin mai koyarwa Pep Guardiola Sai dai wani sauyi da aka samu a kakar wasa ta bana ta 2022 zuwa 2023, kungiyoyi za su iya sauya ‘yan wasa biyar maimakon uku da ake yi a baya kuma za’a iya sauya ‘yan wasa uku a minti 45 din farko, sannan a saka sauran a zagaye na biyu, domin a rage bata lokaci idan ana buga wasa.

  • 2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?
  • Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Sannan wannan shi ne karon farko da za’a fara canja ‘yan kwallo biyar a gasar Premier League, bayan da tuni Bundesliga da Ligue 1 da Primeir Liga da La Liga da kuma Serie A suka dade da irin wannan tsarin.

Haka kuma a kakar nan za’a buga gasar kofin duniya da kasar Katar za ta karbi bakunci tsakanin watan Nuwamba zuwa cikin watan Disamba saboda haka za’a yi hutu a Premier a mako na12 ko na 13 ga watan Nuwamba zuwa 26 ga watan Disambar, domin gasar ta cin kofin duniya.

Har ila yau, wani canji da aka samu shi ne kyaftin-kyaftin din kungiyoyin Premier League sun amince cewar ba duk wasa ne za su ci gaba da sa gwiwa daya a kasa ba daga kakar nan, domin goyon bayan yaki da wariwar launin fata.

Labarai Masu Nasaba

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

An dai amince cewa za’a iya yi a farkon bude gasar ko lokacin rufe ta ko wani babban wasa a Ingila, shima ba wai ya zama wajibi ba sai dai kuma kungiyoyin sun yi kira da babbar murya cewar suna yaki da wariyar launin fata da duk wani nau’in cin zarafi a fannin kwallon kafa.

Kamar yadda aka sani kungiyoyi 20 ne suke buga gasar Premier League, inda 17 daga bara za su hadu da ukun da suka samu gurbin fafatawa a kakar bana daga Championship kuma wadanda suka hauro zuwa Premier League sun hada da Fulham, wadda ta yi kaka daya rabonta da gasar da Bournemouth kaka biyu rabonta da wasannin da Nottingham Forest, wadda shekara 23 rabonta da Premier League.

Gibin shekara 23 rabon da kungiya ta koma buga Premier League da Nottingham ta yi shi ne har yanzu mai tsawo a tarihi da ake da shi, bayan barin gasar kuma kungiyoyi ukun sun maye gurbin Burnley, wadda ta yi kakar wasa shida a Premier League da Watford da kuma Norwich City, wadanda suka yi kaka daya a wasannin da aka karkare a bara.

Da yake ranar 5 ga watan Agusta aka fara kakar wasan Premier League ta 2022/23, inda aka fara da kece raini tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace da Arsenal a filin wasa na Selhust Park dake birnin Landan, Arsenal ce ta samu nasara da ci 2-1.

Tuni kungiyoyi 20 da za su fafata a kakar bana suka daura aniyar yadda za su taka rawar gani a babbar gasar ta Ingila ta bana domin tuni wasu da dama sun sayo sababbin ‘yan wasa domin kara bunkasa kwazonsu, yayin da wasu suka buga wasannin sada zumunta.

A bana Nottingham Forest wadda rabon da ta buga Premier League tun bayan shekara 23, ita ce kan gaba da ta dauki ‘yan kwallo 13 kawo wannan lokacin sai dai ita kuwa Leicester City kawo yanzu ba ta sayi dan kwallo ko daya ba, watakila ta dauka nan gaba.

Kungiyoyin Manchester City da Liberpool su ne wadanda ake ganin kamar sun yi ciniki mai kyau ganin yadda City, wadda ita ce mai kare kambu ta dauki dan wasa Erling Haaland ita kuwa Liberpool Darwin Nunez ta dauka daga Benfica.

Duka kungiyoyin da suke buga gasar dai sun yi iya yinsu wajen ganin sun kara karfi domin tunkarar wannan kakar da za’a shiga sati na biyu a gobe, sai dai abin tambayar a nan shi ne wacce kungiya ce za ta lashe gasar ta bana?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalChelseaFirimiyar IngilaKungiyoyiLiverpoolManchester CityManchester United
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

Next Post

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Related

Dan Nijeriya Lookman Na Kan Gaba Wajen Lashe Kyautar Gwarzon Kwallon Kafa Na Afrika Ta Bana
Wasanni

Atalanta Na Neman Yuro Miliyan 50 Daga Duk Kungiyar Da Ke Son Daukar Lookman

24 hours ago
UEFA
Wasanni

‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai

2 days ago
Muhammad Salah: Gwarzon Afirka A Firimiyar Ingila
Wasanni

Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila

3 days ago
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
Wasanni

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

4 days ago
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
Wasanni

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

5 days ago
Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
Wasanni

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa

5 days ago
Next Post
Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

Matatar Mai ta Haifa Ta Dakatar Da Ayyukanta Bayan Harin Iran

June 17, 2025
Sirikin Buhari Ya Fice Daga Jam’iyyar APC A Kaduna

Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas

June 17, 2025
Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

Sabon Shirin Gwamnatin Katsina: Za A Fara Sauya Tunanin Tubabbun ‘Yan Bindiga

June 17, 2025
‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matasa 51 da Ake Zargi Da Faɗan Daba A Kano

June 17, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

Ministan Waje: Kwakkwaran Zumunci Da Ake Sadawa Da Sin Ya Yi Tasiri Mai Kyau Ga Al’ummar Rwanda

June 16, 2025
Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

Sarkin Musulmi Ya Nuna Baƙin Ciki Kan Kisan Kiyashi A Binuwe

June 16, 2025
Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

Hada-hadar Tattalin Arzikin Sin Ta Gudana Bisa Daidaito A Watan Mayu

June 16, 2025
Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

Sin Ta Fatattaki Laifukan Zamba Ta Shafin Intanet 294,000 A Bara

June 16, 2025
Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake

June 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.