• Leadership Hausa
Tuesday, May 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?

by Abba Ibrahim Wada
10 months ago
in Wasanni
0
Wacce Kungiya Za Ta Lashe Firimiyar Ingila?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kawo yanzu za a iya cewa wasanni za su kankama bayan da tun a ranar Juma’a, 5 ga watan Agustan 2022 aka fara buga wasannin gasar Premier League ta bana, kakar wasa ta 2022 zuwa 2023.

Idan mai karatu bai manta ba, a kakar da ta gabata kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ce ta lashe gasar, kuma biyu a jere da ta lashe wato a 2020 da 2021 da kuma ta 2021 da 2022 a karkashin mai koyarwa Pep Guardiola Sai dai wani sauyi da aka samu a kakar wasa ta bana ta 2022 zuwa 2023, kungiyoyi za su iya sauya ‘yan wasa biyar maimakon uku da ake yi a baya kuma za’a iya sauya ‘yan wasa uku a minti 45 din farko, sannan a saka sauran a zagaye na biyu, domin a rage bata lokaci idan ana buga wasa.

  • 2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?
  • Wike Ga Atiku : Kar Ka Zarge Ni In Ka Fadi A Zabe

Sannan wannan shi ne karon farko da za’a fara canja ‘yan kwallo biyar a gasar Premier League, bayan da tuni Bundesliga da Ligue 1 da Primeir Liga da La Liga da kuma Serie A suka dade da irin wannan tsarin.

Haka kuma a kakar nan za’a buga gasar kofin duniya da kasar Katar za ta karbi bakunci tsakanin watan Nuwamba zuwa cikin watan Disamba saboda haka za’a yi hutu a Premier a mako na12 ko na 13 ga watan Nuwamba zuwa 26 ga watan Disambar, domin gasar ta cin kofin duniya.

Har ila yau, wani canji da aka samu shi ne kyaftin-kyaftin din kungiyoyin Premier League sun amince cewar ba duk wasa ne za su ci gaba da sa gwiwa daya a kasa ba daga kakar nan, domin goyon bayan yaki da wariwar launin fata.

Labarai Masu Nasaba

Haaland Ya Kafa Tarihi A Gasar Firimiya Ta Bana 

Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Man City Burki?

An dai amince cewa za’a iya yi a farkon bude gasar ko lokacin rufe ta ko wani babban wasa a Ingila, shima ba wai ya zama wajibi ba sai dai kuma kungiyoyin sun yi kira da babbar murya cewar suna yaki da wariyar launin fata da duk wani nau’in cin zarafi a fannin kwallon kafa.

Kamar yadda aka sani kungiyoyi 20 ne suke buga gasar Premier League, inda 17 daga bara za su hadu da ukun da suka samu gurbin fafatawa a kakar bana daga Championship kuma wadanda suka hauro zuwa Premier League sun hada da Fulham, wadda ta yi kaka daya rabonta da gasar da Bournemouth kaka biyu rabonta da wasannin da Nottingham Forest, wadda shekara 23 rabonta da Premier League.

Gibin shekara 23 rabon da kungiya ta koma buga Premier League da Nottingham ta yi shi ne har yanzu mai tsawo a tarihi da ake da shi, bayan barin gasar kuma kungiyoyi ukun sun maye gurbin Burnley, wadda ta yi kakar wasa shida a Premier League da Watford da kuma Norwich City, wadanda suka yi kaka daya a wasannin da aka karkare a bara.

Da yake ranar 5 ga watan Agusta aka fara kakar wasan Premier League ta 2022/23, inda aka fara da kece raini tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace da Arsenal a filin wasa na Selhust Park dake birnin Landan, Arsenal ce ta samu nasara da ci 2-1.

Tuni kungiyoyi 20 da za su fafata a kakar bana suka daura aniyar yadda za su taka rawar gani a babbar gasar ta Ingila ta bana domin tuni wasu da dama sun sayo sababbin ‘yan wasa domin kara bunkasa kwazonsu, yayin da wasu suka buga wasannin sada zumunta.

A bana Nottingham Forest wadda rabon da ta buga Premier League tun bayan shekara 23, ita ce kan gaba da ta dauki ‘yan kwallo 13 kawo wannan lokacin sai dai ita kuwa Leicester City kawo yanzu ba ta sayi dan kwallo ko daya ba, watakila ta dauka nan gaba.

Kungiyoyin Manchester City da Liberpool su ne wadanda ake ganin kamar sun yi ciniki mai kyau ganin yadda City, wadda ita ce mai kare kambu ta dauki dan wasa Erling Haaland ita kuwa Liberpool Darwin Nunez ta dauka daga Benfica.

Duka kungiyoyin da suke buga gasar dai sun yi iya yinsu wajen ganin sun kara karfi domin tunkarar wannan kakar da za’a shiga sati na biyu a gobe, sai dai abin tambayar a nan shi ne wacce kungiya ce za ta lashe gasar ta bana?

Tags: ArsenalChelseaFirimiyar IngilaKungiyoyiLiverpoolManchester CityManchester United
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Gudunmawar Naira Biliyan 2.5 Don Kammala Aikin Tashar Tsandauri

Next Post

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Related

Haaland Ya Kafa Tarihi A Gasar Firimiya Ta Bana 
Wasanni

Haaland Ya Kafa Tarihi A Gasar Firimiya Ta Bana 

2 days ago
Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Man City Burki?
Wasanni

Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Man City Burki?

3 days ago
La liga Ta Zama Dandalin Masu Nuna Wariya, Cewar Vinicius
Wasanni

La liga Ta Zama Dandalin Masu Nuna Wariya, Cewar Vinicius

3 days ago
Ban Ji Dadin Rashin Zuwa Gasar Zakarun Turai A Badi Ba -Salah
Wasanni

Ban Ji Dadin Rashin Zuwa Gasar Zakarun Turai A Badi Ba -Salah

3 days ago
Jordi Alba Zai Bar Barcelona A Karshen Kakar Bana 
Wasanni

Jordi Alba Zai Bar Barcelona A Karshen Kakar Bana 

5 days ago
Saka Ya Kara Kwantiragin Shekaru 4 A Arsenal 
Wasanni

Saka Ya Kara Kwantiragin Shekaru 4 A Arsenal 

6 days ago
Next Post
Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

Damfarar Miliyan 66: Kotu Ta Daure Maman Boko Haram Da Wasu Mutum 2

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Tuntuba Tare Da Musayar Ra’ayi Da Dukkan Bangarori Game Da Warware Rikicin Ukraine A Siyasance

Kasar Sin Ta Tuntuba Tare Da Musayar Ra’ayi Da Dukkan Bangarori Game Da Warware Rikicin Ukraine A Siyasance

May 29, 2023
Sin Da Afirka Sun Fi Bukatar Kara Hadin Gwiwa Da Juna

Sin Da Afirka Sun Fi Bukatar Kara Hadin Gwiwa Da Juna

May 29, 2023
Tinubu Ya Taya Erdoğan Murnar Nasarar Cin Zaben Shugaban Kasar Turkiyya

Tinubu Ya Taya Erdoğan Murnar Nasarar Cin Zaben Shugaban Kasar Turkiyya

May 29, 2023
Sabon Gwamnan Sakkwato Ahmed Aliyu Ya Nemi Goyon Bayan ‘Yan Adawa A Jihar

Sabon Gwamnan Sakkwato Ahmed Aliyu Ya Nemi Goyon Bayan ‘Yan Adawa A Jihar

May 29, 2023
An Wallafa Littafi Kan Jawabin Shugaba Xi Jinping A Wajen Taron Kolin Kasar Sin Da Yankin Tsakiyar Asiya

An Wallafa Littafi Kan Jawabin Shugaba Xi Jinping A Wajen Taron Kolin Kasar Sin Da Yankin Tsakiyar Asiya

May 29, 2023
Mamallakin Tashar Talebijin Ta AIT, Raymond Dokpesi Ya Rasu A Abuja

Mamallakin Tashar Talebijin Ta AIT, Raymond Dokpesi Ya Rasu A Abuja

May 29, 2023
Za A Harba Kumbon Shenzhou-16 A Gobe Talata

Za A Harba Kumbon Shenzhou-16 A Gobe Talata

May 29, 2023
Ya Dace Amurka Ta Koyi Hikimomin Kissinger Don Yin Mu’amala Da Kasar Sin

Ya Dace Amurka Ta Koyi Hikimomin Kissinger Don Yin Mu’amala Da Kasar Sin

May 29, 2023
An Kammala Bikin Baje Kolin Fasahohin Tattara Manyan Bayanai Na Kasa Da Kasa Na Sin

An Kammala Bikin Baje Kolin Fasahohin Tattara Manyan Bayanai Na Kasa Da Kasa Na Sin

May 29, 2023
Jagoranci Za Mu Yi Ba Mulkin ‘Yan Nijeriya Ba – Tinubu

Abubuwa 5 Da Gwamnatin Tinubu Za Ta Mayar Da Hankali Kan Su

May 29, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.