ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zabe

A ranar 31 ga watan Yuli ne, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana kammala rajistar mallakar katin zabe da ta bude a ranar 28 ga Yunin 2020, shekara biyu kenan da wata guda. 

Bayan kammala rajistar, hukumar ta ce ta yi sabbin rajista ga ‘yan Nijeriya miliyan 12, 298, 944. Kafin nan akwai masu rajista har mutum 84, 000, 484.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wato a yanzu akwai wadanda suka mallaki katin zabe har miliyan 96, 299, 428 kenan.

ADVERTISEMENT

A bayanan da hukumar INEC ta fitar har yanzu Kano da Legas ke da mafi yawan masu rajista.

Jihohi uku da ke kan gaba wajen yawan wadanda suka yi rajista kwanan nan, sun hada da Legas da ke da mutum 585,629.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Sai Kano mai 569, 103. Ta uku it ace Jihar Delta mai mutum 523, 517. Jihohi masu karancin wadanda suka yi rajista kwanan nan su ne: Ekiti da ke da mutum 124, 844.

Mai bi mata ita ce Jihar Yobe mai mutum 152, 414. Sai Babban Birnin Tarayya (FCT), Abuja mai mutum 211, 341.

A wannan kididdigan ya nuna cewa yankin Kudu sun fi yankin Arewa karin masu rajistar, alamu na kuma nuna cewa kowani bangare zai iya yin dan bangarensa ne a zaben 2023.

Amma dai ba a nan gizo ke sakar ba, daga bibiyar yawan masu rajistar zabe, za a fahimci ‘yan takarar jam’iyyar APC da PDP har yanzu su ne a sahun gaban wajen yiwuwar lashe zabe.

Amma fa karfin yunkurowar da Kwankwaso na NNPP da Obi na LP za su iya kawo wa nasarar Atiku cikas sosai.

Haka kuma za su iya hana Tinubu lashe zabe kaitsaye. Sakamakon zaben Ekiti da Osun na gwamna da kuma zabukan cike gurbi na jihohi da tarayya sun nuna APC da PDP dai ne manyan ‘yan takara.

Idan a bi ta barawo, to a bi ta ma bi sahu, kamar yadda masu iya magana suke cewa tun bayan kafuwar jam’iyyar NNPP mai kayan marmari na Kwankwas, gaba daya tasirin jam’iyyar PDP ya mutu a Kano.

Ita kanta jam’iyya mai mulki a Kano ta kasa tsayuwa da kafafuwanta don ta shiga rudani har wasu jiga-jiganta suka shiga NNPP irin su Malam Ibrahim Shekarau, Sanata kuma Tsohon Gwamna a jihar.

Kasancewar a duk arewacin Nijeriya, Jihar Kano ce aka fi samun yawan kuri’u, kenan akwai yiwuwar Kwankwaso zai iya yi wa duk wata jam’iyya illa a jihar.

Masu sharhi kan siyasa sun hasaso cewa duk dan takarar da bai samu nasara a jihohin Kano ko Legas ko Kaduna ba, ko shakka babu zai wahala ya iya samun nasara a zaben 2023 na shugaban kasa.

A Kaduna ma nan ana ganin Gwamna Nasir El-Rufai ya janyo wa jam’iyyar APC bakin jini. Sannan kuma dan Jihar Kaduna ne mataimakin takarar Peter Obi na jam’iyyarr LP; wato Yusuf Datti Baba-Ahmed, ko ba komai a jihar LP za ta iya jan wasu kaso na kuri’u da za a jefa.

Idan aka koma kudu maso kudu kuwa, sanin kowa ne jam’iyyar APC ba ta da wani tasiri a yankin. Mutanen yankin sun so a ce Gwamna Wike ne dan takarar PDP ba Atiku Abubakar ba.

Dalili kenan PDP ta kasa barci tana so sai ta lallashi Gwamna Nysome Wike daga fushin da ya yi. Dama kuma yankin na PDP ne tun filazal.

Haka kuma rashin bai wa dan kudu maso gabas takara da PDP ko APC suka yi, ya sa jihohin Igbo sun karkata ga dansu Peter Obi na jam’iyyar LP.

Idan kuwa aka koma ma’anar siyasa za a ga cewa, siyasa hanya ce da mutane ke bi wajen rayuwa a hade, ko a tare ko a kungiyance cikin manufa daya.

Siyasa na nufin hada yarjejeniya tsakanin mutane domin su zauna tare duk da mabam-bantan ra’ayoyi, kabilu da addinai, a birane da kasashe.

Bisa wannan ta’arifin na siyasa a yanayin da ake tafiya a Nijeriya, kowani bangare ko yanki nasu suke yi.

Kenan yankin kudu sun yunkuro a wannan karo ta la’akari da samun yawan masu rajistan katin zabe. Da can sun san yankin arewa ba yinsu suke yi ba.

Kuma a yanzu yankin arewa za a yi masu illa game da rarrabuwan ‘yan takara da aka samu a yankin. Ko ma dai mene ne, Hausawa na cewa ‘ba a san ma ci tuwo ba, sai miya ta kare’.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Martanin El-Rufa'i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.