ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Zabe

A ranar 31 ga watan Yuli ne, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana kammala rajistar mallakar katin zabe da ta bude a ranar 28 ga Yunin 2020, shekara biyu kenan da wata guda. 

Bayan kammala rajistar, hukumar ta ce ta yi sabbin rajista ga ‘yan Nijeriya miliyan 12, 298, 944. Kafin nan akwai masu rajista har mutum 84, 000, 484.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wato a yanzu akwai wadanda suka mallaki katin zabe har miliyan 96, 299, 428 kenan.

ADVERTISEMENT

A bayanan da hukumar INEC ta fitar har yanzu Kano da Legas ke da mafi yawan masu rajista.

Jihohi uku da ke kan gaba wajen yawan wadanda suka yi rajista kwanan nan, sun hada da Legas da ke da mutum 585,629.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sai Kano mai 569, 103. Ta uku it ace Jihar Delta mai mutum 523, 517. Jihohi masu karancin wadanda suka yi rajista kwanan nan su ne: Ekiti da ke da mutum 124, 844.

Mai bi mata ita ce Jihar Yobe mai mutum 152, 414. Sai Babban Birnin Tarayya (FCT), Abuja mai mutum 211, 341.

A wannan kididdigan ya nuna cewa yankin Kudu sun fi yankin Arewa karin masu rajistar, alamu na kuma nuna cewa kowani bangare zai iya yin dan bangarensa ne a zaben 2023.

Amma dai ba a nan gizo ke sakar ba, daga bibiyar yawan masu rajistar zabe, za a fahimci ‘yan takarar jam’iyyar APC da PDP har yanzu su ne a sahun gaban wajen yiwuwar lashe zabe.

Amma fa karfin yunkurowar da Kwankwaso na NNPP da Obi na LP za su iya kawo wa nasarar Atiku cikas sosai.

Haka kuma za su iya hana Tinubu lashe zabe kaitsaye. Sakamakon zaben Ekiti da Osun na gwamna da kuma zabukan cike gurbi na jihohi da tarayya sun nuna APC da PDP dai ne manyan ‘yan takara.

Idan a bi ta barawo, to a bi ta ma bi sahu, kamar yadda masu iya magana suke cewa tun bayan kafuwar jam’iyyar NNPP mai kayan marmari na Kwankwas, gaba daya tasirin jam’iyyar PDP ya mutu a Kano.

Ita kanta jam’iyya mai mulki a Kano ta kasa tsayuwa da kafafuwanta don ta shiga rudani har wasu jiga-jiganta suka shiga NNPP irin su Malam Ibrahim Shekarau, Sanata kuma Tsohon Gwamna a jihar.

Kasancewar a duk arewacin Nijeriya, Jihar Kano ce aka fi samun yawan kuri’u, kenan akwai yiwuwar Kwankwaso zai iya yi wa duk wata jam’iyya illa a jihar.

Masu sharhi kan siyasa sun hasaso cewa duk dan takarar da bai samu nasara a jihohin Kano ko Legas ko Kaduna ba, ko shakka babu zai wahala ya iya samun nasara a zaben 2023 na shugaban kasa.

A Kaduna ma nan ana ganin Gwamna Nasir El-Rufai ya janyo wa jam’iyyar APC bakin jini. Sannan kuma dan Jihar Kaduna ne mataimakin takarar Peter Obi na jam’iyyarr LP; wato Yusuf Datti Baba-Ahmed, ko ba komai a jihar LP za ta iya jan wasu kaso na kuri’u da za a jefa.

Idan aka koma kudu maso kudu kuwa, sanin kowa ne jam’iyyar APC ba ta da wani tasiri a yankin. Mutanen yankin sun so a ce Gwamna Wike ne dan takarar PDP ba Atiku Abubakar ba.

Dalili kenan PDP ta kasa barci tana so sai ta lallashi Gwamna Nysome Wike daga fushin da ya yi. Dama kuma yankin na PDP ne tun filazal.

Haka kuma rashin bai wa dan kudu maso gabas takara da PDP ko APC suka yi, ya sa jihohin Igbo sun karkata ga dansu Peter Obi na jam’iyyar LP.

Idan kuwa aka koma ma’anar siyasa za a ga cewa, siyasa hanya ce da mutane ke bi wajen rayuwa a hade, ko a tare ko a kungiyance cikin manufa daya.

Siyasa na nufin hada yarjejeniya tsakanin mutane domin su zauna tare duk da mabam-bantan ra’ayoyi, kabilu da addinai, a birane da kasashe.

Bisa wannan ta’arifin na siyasa a yanayin da ake tafiya a Nijeriya, kowani bangare ko yanki nasu suke yi.

Kenan yankin kudu sun yunkuro a wannan karo ta la’akari da samun yawan masu rajistan katin zabe. Da can sun san yankin arewa ba yinsu suke yi ba.

Kuma a yanzu yankin arewa za a yi masu illa game da rarrabuwan ‘yan takara da aka samu a yankin. Ko ma dai mene ne, Hausawa na cewa ‘ba a san ma ci tuwo ba, sai miya ta kare’.

Zabe
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Martanin El-Rufa'i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.