• English
  • Business News
Saturday, June 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
2023: Ko Yawan Masu Rajistar Zabe Zai Iya Tasiri Ga ‘Yan Takara?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 31 ga watan Yuli ne, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana kammala rajistar mallakar katin zabe da ta bude a ranar 28 ga Yunin 2020, shekara biyu kenan da wata guda. 

Bayan kammala rajistar, hukumar ta ce ta yi sabbin rajista ga ‘yan Nijeriya miliyan 12, 298, 944. Kafin nan akwai masu rajista har mutum 84, 000, 484.

  • Shugaba Buhari Zai Kawo Karshen Rashin Tsaro A Nijeriya -Buratai
  • Ziyarar Babbar jami’ar Lithuania A Taiwan Shirme Ne

Wato a yanzu akwai wadanda suka mallaki katin zabe har miliyan 96, 299, 428 kenan.

A bayanan da hukumar INEC ta fitar har yanzu Kano da Legas ke da mafi yawan masu rajista.

Jihohi uku da ke kan gaba wajen yawan wadanda suka yi rajista kwanan nan, sun hada da Legas da ke da mutum 585,629.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

Sai Kano mai 569, 103. Ta uku it ace Jihar Delta mai mutum 523, 517. Jihohi masu karancin wadanda suka yi rajista kwanan nan su ne: Ekiti da ke da mutum 124, 844.

Mai bi mata ita ce Jihar Yobe mai mutum 152, 414. Sai Babban Birnin Tarayya (FCT), Abuja mai mutum 211, 341.

A wannan kididdigan ya nuna cewa yankin Kudu sun fi yankin Arewa karin masu rajistar, alamu na kuma nuna cewa kowani bangare zai iya yin dan bangarensa ne a zaben 2023.

Amma dai ba a nan gizo ke sakar ba, daga bibiyar yawan masu rajistar zabe, za a fahimci ‘yan takarar jam’iyyar APC da PDP har yanzu su ne a sahun gaban wajen yiwuwar lashe zabe.

Amma fa karfin yunkurowar da Kwankwaso na NNPP da Obi na LP za su iya kawo wa nasarar Atiku cikas sosai.

Haka kuma za su iya hana Tinubu lashe zabe kaitsaye. Sakamakon zaben Ekiti da Osun na gwamna da kuma zabukan cike gurbi na jihohi da tarayya sun nuna APC da PDP dai ne manyan ‘yan takara.

Idan a bi ta barawo, to a bi ta ma bi sahu, kamar yadda masu iya magana suke cewa tun bayan kafuwar jam’iyyar NNPP mai kayan marmari na Kwankwas, gaba daya tasirin jam’iyyar PDP ya mutu a Kano.

Ita kanta jam’iyya mai mulki a Kano ta kasa tsayuwa da kafafuwanta don ta shiga rudani har wasu jiga-jiganta suka shiga NNPP irin su Malam Ibrahim Shekarau, Sanata kuma Tsohon Gwamna a jihar.

Kasancewar a duk arewacin Nijeriya, Jihar Kano ce aka fi samun yawan kuri’u, kenan akwai yiwuwar Kwankwaso zai iya yi wa duk wata jam’iyya illa a jihar.

Masu sharhi kan siyasa sun hasaso cewa duk dan takarar da bai samu nasara a jihohin Kano ko Legas ko Kaduna ba, ko shakka babu zai wahala ya iya samun nasara a zaben 2023 na shugaban kasa.

A Kaduna ma nan ana ganin Gwamna Nasir El-Rufai ya janyo wa jam’iyyar APC bakin jini. Sannan kuma dan Jihar Kaduna ne mataimakin takarar Peter Obi na jam’iyyarr LP; wato Yusuf Datti Baba-Ahmed, ko ba komai a jihar LP za ta iya jan wasu kaso na kuri’u da za a jefa.

Idan aka koma kudu maso kudu kuwa, sanin kowa ne jam’iyyar APC ba ta da wani tasiri a yankin. Mutanen yankin sun so a ce Gwamna Wike ne dan takarar PDP ba Atiku Abubakar ba.

Dalili kenan PDP ta kasa barci tana so sai ta lallashi Gwamna Nysome Wike daga fushin da ya yi. Dama kuma yankin na PDP ne tun filazal.

Haka kuma rashin bai wa dan kudu maso gabas takara da PDP ko APC suka yi, ya sa jihohin Igbo sun karkata ga dansu Peter Obi na jam’iyyar LP.

Idan kuwa aka koma ma’anar siyasa za a ga cewa, siyasa hanya ce da mutane ke bi wajen rayuwa a hade, ko a tare ko a kungiyance cikin manufa daya.

Siyasa na nufin hada yarjejeniya tsakanin mutane domin su zauna tare duk da mabam-bantan ra’ayoyi, kabilu da addinai, a birane da kasashe.

Bisa wannan ta’arifin na siyasa a yanayin da ake tafiya a Nijeriya, kowani bangare ko yanki nasu suke yi.

Kenan yankin kudu sun yunkuro a wannan karo ta la’akari da samun yawan masu rajistan katin zabe. Da can sun san yankin arewa ba yinsu suke yi ba.

Kuma a yanzu yankin arewa za a yi masu illa game da rarrabuwan ‘yan takara da aka samu a yankin. Ko ma dai mene ne, Hausawa na cewa ‘ba a san ma ci tuwo ba, sai miya ta kare’.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 2023Kuri'aMasu Kada Kuri'aShugabanniSiyasaTambarin DimokuradiyyaZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Salman Rushdie: Wanda Ya Yi Batanci Ga Annabi Na Cikin Mawuyacin Hali Bayan Kai Masa Hari

Next Post

Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Related

Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

7 days ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

2 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

3 weeks ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

3 weeks ago
Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

1 month ago
Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

1 month ago
Next Post
Martanin El-Rufa’i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

Martanin El-Rufa'i: Ko Gawata Ba Za Ta Kusanci PDP Ba

LABARAI MASU NASABA

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin

June 13, 2025
jam'iyyu

Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya

June 13, 2025
Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai

June 13, 2025
Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

Babban Jami’in Diflomasiyyar Kasar Sin Ya Yi Kiran Karfafa Alaka Da Afirka

June 13, 2025
Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

Xi Ya Yi Kira Da A Kara Azamar Gina Kasa A Gabar Da Ake Bikin Cika Shekaru 120 Da Haihuwar Dan Mazan Jiya Chen Yun

June 13, 2025
Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

June 13, 2025
Nijeriya Da Morocco Za Su Sanya Hannu Kan Kulla Yarjejeniyar Aikin Bututun Iskar Gas

Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida

June 13, 2025
Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka

June 13, 2025
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

June 13, 2025
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi

June 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.