• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

Ziyarar masu yawon bude ido zuwa tsaunukan Maghreb a baya ta kasance wata kafar samun kudaden shiga da ayyukan yi a yankin da ke fama da fatara.

Makonnin baya, kafin aukuwar ibtila’in girgizar kasar da ta girgiza Morocco, Abdessamad Elgzouli ya kan jagoranci mutane masu zuwa kasar yawon bude ido, inda yake jagorantar su zuwa tsaunukan kasar dake yankin al’ummomin Maghreb kuma matsugunin kabilar Berber ko kuma Amazigh.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

Yanzu sabuwar sana’ar Elgzouli ita ce taimakawa wajen kafa rumfuna a sansanoni a Amizmiz, inda daruruwan mutanen da suka rasa muhallansu a sakamakon girgizar kasar da ta auku cikin wannan watan su ke.

Elgzouli wanda yake kewaye cikin gidan shi wanda ya lalace duk da cewa bai rushe ba, ya ce, abin da ya wuce ya zama tarihi”.

Girgizar kasar mai karfin 6.8 a ma’auni ta kashe akalla mutum 3,000, ta kuma shafe gidaje a kauyukan da ke tsaunukan, kana ta lalata makarantu, asibitoci da gidaje a gundumomi 5 da lamarin ya fi shafa. Cikin ‘yan dakikai ta shafe tushen tattalin arzikin kasar na yawon bude ido wanda al’ummomin na Moropcco masu fama da talauci da karancin ci gaba suke alfahari da shi wajen samun kudaden shiga.

Yanzu yankin yana fuskantar matsalar sake farfado da gine-ginen da suka rushe a daidai sa’adda ake tunkarar yanayi mai tsanani na hunturu wanda zai sa aikin farfadowar ya yi matukar wuya sannan kuma ya dada ta’azzara matsin rayuwa ga dubban ‘yan Marocco da ke rayuwa a cikin rumfunan da aka kafa a can tudun tsaunnukan.

Yayin da gwamnatin kasar ta yi alkawarin zuba tsabar kudi dala biliyan $11.7 da zummar taimaka wa mutanen da girgizar kasar ta shafa su miliyan 4 sake farfado da rayuwarsu, kwararru sun ce matsalar kai dauki ta habaka fiye da haka yadda ake tsammani. Tun farkon watan nan dai, wani binciken Amurka kan yanayi ya kiyasta ibtila’in cewa zai dada tsananta tabarbarewar arzikin kasa, kana ta yiwu ta lakume wa kasar kaso 8 daga kudaden shigar Morocco.

Baya ga haka kuma, ibtila’in ya dau wani salon siyasa yayin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da karbar taimakon jinkai daga kasashe kamar makwabciyarta kuma abokiyar hammayarta, Algeria, da kuma iyayen mulkin mallakarta Faransa, kana, ta amince da taimakon wasu tsirarun kasashe kawai. Masu suka sun ce hukumomi sun yi jan kafa wajen daukar mataki.

Sarkin Morocco Muhammad na BI yana birnin Paris a lokacin da girgizar kasar ta auku. Kwanaki bayan nan kuma ya ziyarci asibitoci dake biranen Marakesh da ibtila’in ya lalata.

Hukumomi sun kalubalanci sukar da ake musu sannan ‘yan Morocco sun bayyana martanin sakin da hukumomin kasar da girman kai. Kana sun nuna irin kayayyakin da aka taimaka musu da su kamar sutura, barguna, abinci da magunguna daga kasashe a fadin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maddison Ba Zai Buga Wasansu Da Liverpool Ba Saboda Raunin Da Ya Samu

Next Post

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Related

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa
Kasashen Ketare

An Tsare Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Cin Hanci Da Rashawa

3 days ago
An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati
Kasashen Ketare

An Kama Tsohon Firaministan Mali Bisa Zargin Karkatar Da Dukiyar Gwamnati

1 week ago
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
Kasashen Ketare

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

2 weeks ago
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?
Kasashen Ketare

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

3 weeks ago
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa
Kasashen Ketare

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

3 weeks ago
Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza
Kasashen Ketare

Faransa Za Ta Fara Jefa Kayan Agaji Ta Sama A Gaza

3 weeks ago
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

LABARAI MASU NASABA

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

2027: ‘Yan Siyasa Sun Yi Watsi Da Gargadin INEC, Sun Ci Gaba Da Yakin Neman Zabe

August 23, 2025
Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

August 23, 2025
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

August 23, 2025
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.