• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Ziyarar masu yawon bude ido zuwa tsaunukan Maghreb a baya ta kasance wata kafar samun kudaden shiga da ayyukan yi a yankin da ke fama da fatara.

Makonnin baya, kafin aukuwar ibtila’in girgizar kasar da ta girgiza Morocco, Abdessamad Elgzouli ya kan jagoranci mutane masu zuwa kasar yawon bude ido, inda yake jagorantar su zuwa tsaunukan kasar dake yankin al’ummomin Maghreb kuma matsugunin kabilar Berber ko kuma Amazigh.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

Yanzu sabuwar sana’ar Elgzouli ita ce taimakawa wajen kafa rumfuna a sansanoni a Amizmiz, inda daruruwan mutanen da suka rasa muhallansu a sakamakon girgizar kasar da ta auku cikin wannan watan su ke.

Elgzouli wanda yake kewaye cikin gidan shi wanda ya lalace duk da cewa bai rushe ba, ya ce, abin da ya wuce ya zama tarihi”.

Girgizar kasar mai karfin 6.8 a ma’auni ta kashe akalla mutum 3,000, ta kuma shafe gidaje a kauyukan da ke tsaunukan, kana ta lalata makarantu, asibitoci da gidaje a gundumomi 5 da lamarin ya fi shafa. Cikin ‘yan dakikai ta shafe tushen tattalin arzikin kasar na yawon bude ido wanda al’ummomin na Moropcco masu fama da talauci da karancin ci gaba suke alfahari da shi wajen samun kudaden shiga.

Yanzu yankin yana fuskantar matsalar sake farfado da gine-ginen da suka rushe a daidai sa’adda ake tunkarar yanayi mai tsanani na hunturu wanda zai sa aikin farfadowar ya yi matukar wuya sannan kuma ya dada ta’azzara matsin rayuwa ga dubban ‘yan Marocco da ke rayuwa a cikin rumfunan da aka kafa a can tudun tsaunnukan.

Yayin da gwamnatin kasar ta yi alkawarin zuba tsabar kudi dala biliyan $11.7 da zummar taimaka wa mutanen da girgizar kasar ta shafa su miliyan 4 sake farfado da rayuwarsu, kwararru sun ce matsalar kai dauki ta habaka fiye da haka yadda ake tsammani. Tun farkon watan nan dai, wani binciken Amurka kan yanayi ya kiyasta ibtila’in cewa zai dada tsananta tabarbarewar arzikin kasa, kana ta yiwu ta lakume wa kasar kaso 8 daga kudaden shigar Morocco.

Baya ga haka kuma, ibtila’in ya dau wani salon siyasa yayin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da karbar taimakon jinkai daga kasashe kamar makwabciyarta kuma abokiyar hammayarta, Algeria, da kuma iyayen mulkin mallakarta Faransa, kana, ta amince da taimakon wasu tsirarun kasashe kawai. Masu suka sun ce hukumomi sun yi jan kafa wajen daukar mataki.

Sarkin Morocco Muhammad na BI yana birnin Paris a lokacin da girgizar kasar ta auku. Kwanaki bayan nan kuma ya ziyarci asibitoci dake biranen Marakesh da ibtila’in ya lalata.

Hukumomi sun kalubalanci sukar da ake musu sannan ‘yan Morocco sun bayyana martanin sakin da hukumomin kasar da girman kai. Kana sun nuna irin kayayyakin da aka taimaka musu da su kamar sutura, barguna, abinci da magunguna daga kasashe a fadin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maddison Ba Zai Buga Wasansu Da Liverpool Ba Saboda Raunin Da Ya Samu

Next Post

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Related

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa
Kasashen Ketare

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

2 days ago
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta
Kasashen Ketare

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

2 weeks ago
Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 
Kasashen Ketare

Trump Zai Shirya Liyafar Musamman Ga Manyan Ƴan Crypto 

2 weeks ago
Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci
Kasashen Ketare

Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa

3 weeks ago
Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali
Kasashen Ketare

Sarkin Saudiyya Ya Ɗauki Nauyin Falasɗinawa 1,000 Su Sauke Farali

3 weeks ago
Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar
Kasashen Ketare

Birtaniya Ta Fitar Da Sabbin Tsauraran Dokokin Zama A Ƙasar

3 weeks ago
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.