• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Kasashen Ketare
0
Wace Irin Asara Girgizar Kasa Ta Haifar A Maroko?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Ziyarar masu yawon bude ido zuwa tsaunukan Maghreb a baya ta kasance wata kafar samun kudaden shiga da ayyukan yi a yankin da ke fama da fatara.

Makonnin baya, kafin aukuwar ibtila’in girgizar kasar da ta girgiza Morocco, Abdessamad Elgzouli ya kan jagoranci mutane masu zuwa kasar yawon bude ido, inda yake jagorantar su zuwa tsaunukan kasar dake yankin al’ummomin Maghreb kuma matsugunin kabilar Berber ko kuma Amazigh.

  • A Shirye Sin Take Ta Inganta Hadin Gwiwa Da UNESCO Domin Samar Da Ci Gaba Da Zaman Lafiya A Duniya
  • Manyan Batutuwa 7 Da Za Su Turnike Zauren Majalisa Bayan Dawowa Hutu

Yanzu sabuwar sana’ar Elgzouli ita ce taimakawa wajen kafa rumfuna a sansanoni a Amizmiz, inda daruruwan mutanen da suka rasa muhallansu a sakamakon girgizar kasar da ta auku cikin wannan watan su ke.

Elgzouli wanda yake kewaye cikin gidan shi wanda ya lalace duk da cewa bai rushe ba, ya ce, abin da ya wuce ya zama tarihi”.

Girgizar kasar mai karfin 6.8 a ma’auni ta kashe akalla mutum 3,000, ta kuma shafe gidaje a kauyukan da ke tsaunukan, kana ta lalata makarantu, asibitoci da gidaje a gundumomi 5 da lamarin ya fi shafa. Cikin ‘yan dakikai ta shafe tushen tattalin arzikin kasar na yawon bude ido wanda al’ummomin na Moropcco masu fama da talauci da karancin ci gaba suke alfahari da shi wajen samun kudaden shiga.

Yanzu yankin yana fuskantar matsalar sake farfado da gine-ginen da suka rushe a daidai sa’adda ake tunkarar yanayi mai tsanani na hunturu wanda zai sa aikin farfadowar ya yi matukar wuya sannan kuma ya dada ta’azzara matsin rayuwa ga dubban ‘yan Marocco da ke rayuwa a cikin rumfunan da aka kafa a can tudun tsaunnukan.

Yayin da gwamnatin kasar ta yi alkawarin zuba tsabar kudi dala biliyan $11.7 da zummar taimaka wa mutanen da girgizar kasar ta shafa su miliyan 4 sake farfado da rayuwarsu, kwararru sun ce matsalar kai dauki ta habaka fiye da haka yadda ake tsammani. Tun farkon watan nan dai, wani binciken Amurka kan yanayi ya kiyasta ibtila’in cewa zai dada tsananta tabarbarewar arzikin kasa, kana ta yiwu ta lakume wa kasar kaso 8 daga kudaden shigar Morocco.

Baya ga haka kuma, ibtila’in ya dau wani salon siyasa yayin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da karbar taimakon jinkai daga kasashe kamar makwabciyarta kuma abokiyar hammayarta, Algeria, da kuma iyayen mulkin mallakarta Faransa, kana, ta amince da taimakon wasu tsirarun kasashe kawai. Masu suka sun ce hukumomi sun yi jan kafa wajen daukar mataki.

Sarkin Morocco Muhammad na BI yana birnin Paris a lokacin da girgizar kasar ta auku. Kwanaki bayan nan kuma ya ziyarci asibitoci dake biranen Marakesh da ibtila’in ya lalata.

Hukumomi sun kalubalanci sukar da ake musu sannan ‘yan Morocco sun bayyana martanin sakin da hukumomin kasar da girman kai. Kana sun nuna irin kayayyakin da aka taimaka musu da su kamar sutura, barguna, abinci da magunguna daga kasashe a fadin duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maddison Ba Zai Buga Wasansu Da Liverpool Ba Saboda Raunin Da Ya Samu

Next Post

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Related

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Tsawon Kwana 60 Da Hamas – Trump

3 days ago
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya
Kasashen Ketare

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

6 days ago
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?
Kasashen Ketare

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

1 week ago
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025
Kasashen Ketare

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

1 week ago
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17
Kasashen Ketare

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

1 week ago
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Kasashen Ketare

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

2 weeks ago
Next Post
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika

LABARAI MASU NASABA

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Cike Da Hangen Nesa Da Burikan Samar Da Ci Gaba In Ji Firaministan Kasar Senegal

July 5, 2025
‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027

July 5, 2025
Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70

July 5, 2025
Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC

July 5, 2025
Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

Zan Dade Ban Manta Da Mahaifinmu Ba -Abba Sadau

July 5, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa

July 5, 2025
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

July 5, 2025
Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.