• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Manchester City Birki?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
in Wasanni
0
Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Manchester City Birki?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta lashe Premier League na bana na hudu a jere na shida a kaka bakwai na 10 jimilla bayan nasarar doke West Ham 3-1 a wasan karshe na mako na 38 da suka kara ranar Lahadi a Etihad.

Manchester City ta fara cin kwallo ta hannun ta Phil Foden a minti na biyu da fara wasan, kwallo ta shida da ya zura a raga a bana daga wajen yadi na 18 a kakar bana,
haka kuma shi ne ya kara ta biyu, sannan Rodri ya ci ta uku a wasan, sai West Ham ta zare daya ta hannun Mohammed Kudus saura minti uku su je hutun rabin lokaci.

  • Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero
  • Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

Manchester City ta zama ta farko da ta lashe Premier League na hudu a jere, kuma na shida cikin kaka bakwai a tarihin babbar gasar ta Ingila shekara 135, sannan kungiyar ta lashe kofin bayan wasa 44 a jere a dukkan karawa ba tare da an doke ta ba a dukkan fafatawa da cin wasanni 37 da canjaras bakwai.

Pep Guardiola ya lashe kofin lig na 12 a kaka 15 a matakin koci, mai uku a Barcelona da uku a Bayern Munich da shida a Manchester City wanda babu wani koci da ya hada wannan tarihi cikin ‘yan shekaru marasa yawa.

Dan wasa Erling Haaland ya ci kwallo 64 a wasa 66 a Premier League shi ne kan gaba a wannan bajintar a kaka biyu da ya fara buga babbar gasar Ingila, sannan ya lashe takalmin zinare karo biyu a jere da kwallo 27 a raga, wanda ya zura 36 a bara a Premier League.

Labarai Masu Nasaba

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Dan wasan Sifaniya, Rodri, ya yi wasanni 74 ba tare da an doke Manchester City ba, inda aka ci karawa 58 da shi da canjaras 16, tun bayan da Tottenham ta ci 1-0 a cikin Fabrairun 2023.

Manchester City ta buga wasanni 38 da cin 28 da canjaras 7 da rashin nasara uku da cin kwallo 96 aka zura mata 34 da maki 91 kuma dan wasa Phil Foden ne gwarzon dan wasan Premier League na bana, wanda marubuta labarin wasan kwallon kafa suka zaba a bana.

Foden ya lashe kyautar wanda ya ci kwallo 19 ya bayar da takwas aka zura a raga a babbar gasar ta bana, sannan Manchester City ce kan gaba a yawan cin wasan Premier League, wadda ta yi nasara 28, sai Arsenal ta biyu mai cin karawa 28 da kuma Liberpool mai 24.

Wannan shi ne Premier League na 10 jimilla da Manchester City ta lashe. Wadanda ke kan gaba a yawan lashe Premier League;
Manchester United 20. Liberpool 19. Arsenal 13. Manchester City 9. Eberton 9. Aston Billa 7. Chelsea 6. Sunderland 6. Sheffield Wednesday 4. Newcastle United 4. Blackburn Robers 3. Leeds United 3. Wolberhampton 3. Huddersfield Town 3. Derby County 2. Tottenham 2. Burnley 2. Portsmouth 2. Preston North End 2. Leicester City 1
Nottingham Forest FC 1. Ipswich Town 1. West Bromwich Albion 1. Sheffield United 1


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ArsenalGasar firimiyaMan City
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hukumomin Tsaro A Kano Sun Ƙi Biyayya Ga Umarnin Gwamnan Kano

Next Post

DSS, Sojoji Da Duk Jami’an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

Related

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Wasanni

Ƙoƙarin Ƙungiyoyin Afrika A Gasar Kofin Duniya

17 hours ago
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?
Wasanni

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

20 hours ago
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
Wasanni

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

3 days ago
Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi
Wasanni

Manchester United Da Everton Na Zawarcin Wilfred Ndidi

4 days ago
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
Wasanni

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

5 days ago
Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona
Wasanni

Rashford Na Fatan Buga Ƙwallo Tare Da Lamine Yamal A Barcelona

7 days ago
Next Post
DSS, Sojoji Da Duk Jami’an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

DSS, Sojoji Da Duk Jami'an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.