• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Manchester City Birki?

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
City

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta lashe Premier League na bana na hudu a jere na shida a kaka bakwai na 10 jimilla bayan nasarar doke West Ham 3-1 a wasan karshe na mako na 38 da suka kara ranar Lahadi a Etihad.

Manchester City ta fara cin kwallo ta hannun ta Phil Foden a minti na biyu da fara wasan, kwallo ta shida da ya zura a raga a bana daga wajen yadi na 18 a kakar bana,
haka kuma shi ne ya kara ta biyu, sannan Rodri ya ci ta uku a wasan, sai West Ham ta zare daya ta hannun Mohammed Kudus saura minti uku su je hutun rabin lokaci.

  • Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero
  • Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

Manchester City ta zama ta farko da ta lashe Premier League na hudu a jere, kuma na shida cikin kaka bakwai a tarihin babbar gasar ta Ingila shekara 135, sannan kungiyar ta lashe kofin bayan wasa 44 a jere a dukkan karawa ba tare da an doke ta ba a dukkan fafatawa da cin wasanni 37 da canjaras bakwai.

Pep Guardiola ya lashe kofin lig na 12 a kaka 15 a matakin koci, mai uku a Barcelona da uku a Bayern Munich da shida a Manchester City wanda babu wani koci da ya hada wannan tarihi cikin ‘yan shekaru marasa yawa.

Dan wasa Erling Haaland ya ci kwallo 64 a wasa 66 a Premier League shi ne kan gaba a wannan bajintar a kaka biyu da ya fara buga babbar gasar Ingila, sannan ya lashe takalmin zinare karo biyu a jere da kwallo 27 a raga, wanda ya zura 36 a bara a Premier League.

LABARAI MASU NASABA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

Dan wasan Sifaniya, Rodri, ya yi wasanni 74 ba tare da an doke Manchester City ba, inda aka ci karawa 58 da shi da canjaras 16, tun bayan da Tottenham ta ci 1-0 a cikin Fabrairun 2023.

Manchester City ta buga wasanni 38 da cin 28 da canjaras 7 da rashin nasara uku da cin kwallo 96 aka zura mata 34 da maki 91 kuma dan wasa Phil Foden ne gwarzon dan wasan Premier League na bana, wanda marubuta labarin wasan kwallon kafa suka zaba a bana.

Foden ya lashe kyautar wanda ya ci kwallo 19 ya bayar da takwas aka zura a raga a babbar gasar ta bana, sannan Manchester City ce kan gaba a yawan cin wasan Premier League, wadda ta yi nasara 28, sai Arsenal ta biyu mai cin karawa 28 da kuma Liberpool mai 24.

Wannan shi ne Premier League na 10 jimilla da Manchester City ta lashe. Wadanda ke kan gaba a yawan lashe Premier League;
Manchester United 20. Liberpool 19. Arsenal 13. Manchester City 9. Eberton 9. Aston Billa 7. Chelsea 6. Sunderland 6. Sheffield Wednesday 4. Newcastle United 4. Blackburn Robers 3. Leeds United 3. Wolberhampton 3. Huddersfield Town 3. Derby County 2. Tottenham 2. Burnley 2. Portsmouth 2. Preston North End 2. Leicester City 1
Nottingham Forest FC 1. Ipswich Town 1. West Bromwich Albion 1. Sheffield United 1

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax
Wasanni

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
Wasanni

Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba

November 2, 2025
Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara
Wasanni

Wolves Ta Kori Da Kocinta Vitor Pereira Sakamakon Rashin Nasara

November 2, 2025
Next Post
DSS, Sojoji Da Duk Jami’an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

DSS, Sojoji Da Duk Jami'an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.