ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wace Kungiya Ce Za Ta Iya Taka Wa Manchester City Birki?

by Abba Ibrahim Wada
2 years ago
City

Kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta lashe Premier League na bana na hudu a jere na shida a kaka bakwai na 10 jimilla bayan nasarar doke West Ham 3-1 a wasan karshe na mako na 38 da suka kara ranar Lahadi a Etihad.

Manchester City ta fara cin kwallo ta hannun ta Phil Foden a minti na biyu da fara wasan, kwallo ta shida da ya zura a raga a bana daga wajen yadi na 18 a kakar bana,
haka kuma shi ne ya kara ta biyu, sannan Rodri ya ci ta uku a wasan, sai West Ham ta zare daya ta hannun Mohammed Kudus saura minti uku su je hutun rabin lokaci.

  • Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Kamo Tsohon Sarkin Kano Aminu Ado Bayero
  • Ana Fargabar Shigo Da Shinkafar Da Ta Jima A Ajiye Daga Thailand

Manchester City ta zama ta farko da ta lashe Premier League na hudu a jere, kuma na shida cikin kaka bakwai a tarihin babbar gasar ta Ingila shekara 135, sannan kungiyar ta lashe kofin bayan wasa 44 a jere a dukkan karawa ba tare da an doke ta ba a dukkan fafatawa da cin wasanni 37 da canjaras bakwai.

ADVERTISEMENT

Pep Guardiola ya lashe kofin lig na 12 a kaka 15 a matakin koci, mai uku a Barcelona da uku a Bayern Munich da shida a Manchester City wanda babu wani koci da ya hada wannan tarihi cikin ‘yan shekaru marasa yawa.

Dan wasa Erling Haaland ya ci kwallo 64 a wasa 66 a Premier League shi ne kan gaba a wannan bajintar a kaka biyu da ya fara buga babbar gasar Ingila, sannan ya lashe takalmin zinare karo biyu a jere da kwallo 27 a raga, wanda ya zura 36 a bara a Premier League.

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Dan wasan Sifaniya, Rodri, ya yi wasanni 74 ba tare da an doke Manchester City ba, inda aka ci karawa 58 da shi da canjaras 16, tun bayan da Tottenham ta ci 1-0 a cikin Fabrairun 2023.

Manchester City ta buga wasanni 38 da cin 28 da canjaras 7 da rashin nasara uku da cin kwallo 96 aka zura mata 34 da maki 91 kuma dan wasa Phil Foden ne gwarzon dan wasan Premier League na bana, wanda marubuta labarin wasan kwallon kafa suka zaba a bana.

Foden ya lashe kyautar wanda ya ci kwallo 19 ya bayar da takwas aka zura a raga a babbar gasar ta bana, sannan Manchester City ce kan gaba a yawan cin wasan Premier League, wadda ta yi nasara 28, sai Arsenal ta biyu mai cin karawa 28 da kuma Liberpool mai 24.

Wannan shi ne Premier League na 10 jimilla da Manchester City ta lashe. Wadanda ke kan gaba a yawan lashe Premier League;
Manchester United 20. Liberpool 19. Arsenal 13. Manchester City 9. Eberton 9. Aston Billa 7. Chelsea 6. Sunderland 6. Sheffield Wednesday 4. Newcastle United 4. Blackburn Robers 3. Leeds United 3. Wolberhampton 3. Huddersfield Town 3. Derby County 2. Tottenham 2. Burnley 2. Portsmouth 2. Preston North End 2. Leicester City 1
Nottingham Forest FC 1. Ipswich Town 1. West Bromwich Albion 1. Sheffield United 1

City
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Jiya Aka Fara Gasar Cin Kofin Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Real Madrid Ce Tafi Kowacce Kungiya Daraja A Duniya
  • Abba Ibrahim Wada
    Kofin Duniya: Sababbin Dokokin Da FIFA Ta Kawo

MASU ALAKA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
Wasanni

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?
Wasanni

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City
Wasanni

Real Madrid Ta Kammala Ɗaukar Bernardo Silva Daga Man City

June 12, 2026
Next Post
DSS, Sojoji Da Duk Jami’an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

DSS, Sojoji Da Duk Jami'an Tsaro Sun Hallara a Fadar Aminu Ado

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.