• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanda Suka Wawashe Hatsi A Kebbi Sun Shiga Firgici Bayan Kwace Buhun Shinkafa 2,000

by Sulaiman
1 year ago
in Labarai
0
kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar Asabar da ta gabata, tun da sanyin safe matasa da mata da tsoffafi har da matan aure suka far ma sauran buhunan shinkafar Dangote da aka kai tallafi Jihar Kebbi inda suka wawashe akalla buhu dubu biyu.

Bayan samun wannan labarin abin da matasa da sauran jama’a suka aikata jami’an tsaro sun kawo dauki na gaggawa don ganin jama’a ba su wawashe shinkafar ba. Jami’an tsaro sun yi iya kokarisu wajen mai do da shinkafar da aka wawashe.

  • Karin kudin Aikin Hajji: Gwamnatin Kebbi Za Ta Tallafawa Kowanne Maniyyaci Da Naira Miliyan 1
  • Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da Murabus Din Babban Limamin Masallacin Wala

Bayan aukuwar wannan ne, duk dai a ranar da misalin karfe daya na dare jama’a suka sake fitowa suka fasa rumbun ajiyar abincin da karamar hukumar Birnin Kebbi ta ajiye da zimmar rabawa ga jama’arta washe garin ranar Lahadi. A nan ma jami’an tsaron ‘yansanda da na Sojoji sun yi iya kokarinsu na ganin cewa jama’a basu wawashe dukkan abincin ba ta hanyar sanya barkonon tsohuwa amma duk da hakan bai hana aka wawashe wani sashe daga cikin abincin ba.

Yanzu hakan, a Jihar ta kebbi akwai labarin cewa jami’an tsaro sun samu nasarar cafke wasu daga cikin jama’ar da ake zargi da wawashe rumbun da kuma na wata mota a kusa dakasuwar kara da ke cikin garin Birnin Kebbi.

Ganin yadda abin ya auku bi da bi, sai ‘yansanda suka fantsama farautar mutanen da ake zargi da wawashe abincin. Bisa ga hakan hankalin jama’a a garin na Birnin Kebbi ya tashi, inda jama’a da dama suka shiga tsoro da farga.

Labarai Masu Nasaba

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

Bugu da kari, bayan wuni daya an samu zaman lafiya a sassan Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi, sai kuma a washegari, dubban mutane ne suka tattara kansu tare da kutsawa cikin shagunan ‘yan kasuwa masu sayar da shinkafa da sauran hatsi iri-iri a unguwar Bayan-Kara, suka kwashe daruruwan buhuna.

Wani matashi, Abu Wanzan ya bayyana wa wakilinmu cewa, “yunwa da fatara ne suka sa jama’a suka kai hari kan wajen da ake ajiye abinci, haka kuma ba mu ji dadin yadda aka fara raba kayan abinci na baya-bayan nan da gwamnati ta sayo wa al’ummar jihar ba. Da yawa mazauna yankin garin Birnin Kebbi har yanzu ba su amfana da abincin da Gwamna Nasir Idris ya ce za a raba ma jama’a ba.”

Bisa abin da ya faru, ofishin mataimakin gwamnan jihar ya fitar da sanarwa, ta nuna rashin jin dadi game da lamarin tare da bayar da tabbacin cewa an dauki tsauraran matakan tsaro domin dakile sake afkuwar lamarin.

Hakazalika kwamishinan yada labarai da al’adu Alhaji Yakubu Ahmad Birnin Kebbi, ya sanar wa manema labaru da kafa kwamitin mutane 13 a karkashin jagorancin kwamishinan ma’aikatar gona domin gudanar da bincike kan lamarin, wanda gwamnati ta bayyana a matsayin abin takaici da zargi.

Shi ma da yake jawabi ga manema labarai kwamishinan Ma’aikatar aikin goma da albarkatun kasa Alhaji Shehu Mu’azu ya bayyana cewa yawancin shinkafar da aka kwashe daga dakin ajiyar kaya dake Bayan-Kara mallakin karamar hukumar Birnin Kebbi ne a wani bangare na tallafin da gwamnatin jihar ta raba wa Kananan hukumomin 21na jhar.

Ya ce jami’an tsaro sun yi nasarar kwato buhunan abincin sama da 2,000 daga hannun jama’a tare da mayar da su inda aka ajiye su.

Alhaji Shehu Mu’azu wanda shi ne shugaban kwamitin binciken ya shaida wa manema labarai cewa an ba ‘yan kwamitinsa wa’adin kwanaki biyar daga ranar Litinin zuwa Juma’a domin su binciki musabbabin faruwar lamarin, da gano mutane ko kungiyoyin da ke da hannu tare da ba gwamnati shawara yadda ya kamata don kiyaye afkuwar lamarin.

A ranar Alhamis 21 ga watann Maris, ne Gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, ya kaddamar da rabon tallafin abinci da suka hada da shinkafa, Dawa da sauran hatsi domin tausaya wa jama’ar jihar a watan Azumin Ramadan.

Bayan makonni kadan da ya kaddamar da rabon tallafin abincin ne kuma sai Gidauniyar Dangote ta bayyana nata rabon tallafin wanda daga bisani aka daka wawa a ragowar da ba a kai ga rabarwa ba ga al’ummar jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin Manyan Attajiran Nijeriya A 2024

Next Post

Gwamna Uba Ya Umarci Kamo ‘Yan Kwangilar Da Suka Fara Aiki Suka Gudu

Related

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita
Labarai

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

7 hours ago
NNPP
Manyan Labarai

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

9 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Manyan Labarai

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

11 hours ago
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

11 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Labarai

’Yansanda Sun Kama Sojan Gona Da Motocin Sata 3 A Jigawa

14 hours ago
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

16 hours ago
Next Post
Kaduna

Gwamna Uba Ya Umarci Kamo 'Yan Kwangilar Da Suka Fara Aiki Suka Gudu

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.